• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gobara Ta Lakume Kayayyakin Fiye Da Naira Miliyan 70 A Tsohuwar Kasuwar Gombe

by Sadiq
2 years ago
Gobara

Da tsakar daren ranar Larabar da ta gabata ce, gobara ta afku a tsohuwar kasuwar Gombe, wacce ake zargin wasu gungun ‘yan fashi da makami ne suka haddasa, da ta yi sanadin asarar dimbin dukiyar da aka kiyasta ta haura Naira miliyan 70.

Lamarin ya faru ne da misalin karfe 12 na dare a layin teloli, inda wutar ta mamaye shaguna kusan 20 tare da lalata su. Baya ga kadarorin da aka yi asara, ‘yan fashin sun kuma sace kayayyaki na miiyoyin nairori daga shagunan da lamarin ya shafa.

  • Gwamnatin Gombe Za Ta Dauki Sababbin Ma’aikatan Lafiya 200
  • Birnin Jinhua Na Kara Kyautata Alaka Da Kasashen Afirka

Daya daga cikin masu shagunan da lamarin ya shafa, Aminu Abdulrahman, ya bayyana cewa an buga masa waya ne da karfe 1:00 na dare, inda aka sanar da shi ibtila’in wutar.

Ya ce ya yi asarar kekuna dinki guda goma da wasu kayayyaki masu daraja, wadanda aka kiyasta kudinsu ya kai naira miliyan biyu da dubu dari biyar.

Shi ma wani mai shago a tsohuwar kasuwar Gombe Sani Idris, ya bayyana abin da ya faru cikin bakin ciki, inda ya ce shi ma ya samu kiran waya ne da misalin karfe 1 na da re. Ya ce ya yi asarar kekunan dinki biyar da na saka da sauran kayayyaki wanda kudadensu ya kai na naira 800,000.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

Wadanda lamarin ya shafa sun yi kira ga gwamnati da masu hannu da shuni su kai wa wadanda ibtila’in ya shafa dauki gaggawa ddaga wannan mawuyacin hali.

Da yake tsokaci kan wannan mummunan lamari, shugaban kungiyar teloli reshen tsohuwar Kasuwar Gombe, Abu Safwan Muhammad Tukur, ya bayyana kaduwa da alhini kan lamarin.

Ya ce mambobinsu sun yi asarar dukiya mai dimbin yawa da suka hada da kekunan dinki da sauran kayayyaki da kudinsu ya haura naira miliyan 70.

Abu Safwan ya bukaci hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Gombe ta gaggauta kai musu dauki tare da ba da tallafi ga masu shagunan da abin ya shafa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa
Labarai

Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa
Labarai

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina
Labarai

Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

October 22, 2025
Next Post
Maganar Da Na Taba Ji Da Ta Tsorata Ni A Kan Sana’ar Fim – Amina

Maganar Da Na Taba Ji Da Ta Tsorata Ni A Kan Sana’ar Fim - Amina

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

Majalisar NUJ Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 22, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025
Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

Nesa Ta Zo Kusa: Maraba Da Sabon Jirgin Kasa Samfurin CR450 Da Kasar Sin Ta Kera

October 22, 2025
An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

An Sake Saka Sunan Osimhen A Cikin ‘Yan Takarar Kyautar Gwarzon Dan Wasan CAF Na Bana

October 22, 2025
Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

Adadin Yawon Shakatawa Da Mutanen Sin Suka Yi A Cikin Gida Ya Zarce Biliyan 4.998 Tsakanin Janairu Da Satumban Bana

October 22, 2025
Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

Tinubu Ya Amince Da Tallafin Naira 250,000 Ga Ƙananan ’Yan Kasuwa A Jihar Katsina

October 22, 2025
Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

Kasar Sin Ta Sake Farfado Da Muhimman Koguna Da Tafkuna 88 A Kokarin Inganta Muhalli

October 22, 2025
Tanka

Majalisa Ta Buƙaci Gwamnatin Tarayya Ta Kai Agajin Gaggawa Ga Waɗanda Fashewar Tanka Ta Shafa A Neja

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.