ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

ECOWAS Ta Gargadi Sojin Nijar A Kan Hukunta Bazoum

by Sadiq
2 years ago
ECOWAS

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen Afirka ta Yamma (ECOWAS), ta ce ta kadu da jin yunkurin sojoji masu juyin mulki a Nijar na tuhumar zababben shugaban kasa Bazoum Mohamed da zargin babbar cin amanar kasa.

Wata sanarwa da kungiyar ta fitar sa’o’i bayan kalaman sojojin na yi wa Bazoum shari’a, ECOWAS ta ce matakin wani takalar fada ne daga shugabannin sojin.

  • NIS Ta Yi Gargadi Kan Ma Su Balaguro Ta Haramtacciyar Hanya
  • Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano

Ta kuma ce hakan ya ci karo da rahotannin da ake yadawa cewa sabbin masu mulkin Nijar din sun nuna sha’awar bin hanyar masalaha don kawo karshen dambarwar da ake ciki.

ADVERTISEMENT

Sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar sun ce sun tattara isasshiyar shaidar za a iya gurfanar da hambararren shugaban ksar Bazoum Mohamed a gaban kotu, bisa laifin cin amanar kasa.

Sun kuma tuhume shi da yi wa tsaron cikin gida da na wajen kasar, zagon kasa.

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Kakakin sojin Kanal Amadou Abdramane ne, ya bayyana haka a wani jawabi da ya yi ta tashar talbijin ta kasar.

Sojojin na tsare da Bazoum da iyalansa a wani daki na karkashin kasa a fadar gwamnati da ke birnin Yamai, tun bayan hambarar da shi a ranar Lahadi 26 ga watan Yulin bana.

Baya ga shugaban sojojin sun kuma kama wasu daga cikin jiga-jigan gwamnatinsa da ma na jam’iyyarsa ta PNDS Tarayya.

Mai magana da yawun gwamnatin sojin ya ce tuni sun riga ma sun tattara duk wasu bayanai da shaidun da suke bukata domin gurfanar da Bazoum a gaban shari’a.

A sanarwar, kakakin ya ce, za su gurfanar da Bazoum tare da wadanda ya kira masu hada baki da shi a cikin kasar da ma ketare a kan laifukan da suka zayyana, saboda musayar bayanan da ya yi tsakaninsa da wasu ‘yan kasashen waje da shugabannin kasashe da kuma shugabannin kungiyoyin kasashen duniya.

Bayan karbe mulki tare da rushe zababbiyar gwamnatin tuni suka nada majalisar ministoci, tare da yin biris da duk wani kira na neman sasanta rikicin ta hanyar diflomasiyya, daga ECOWAS da sauran kasashe da hukumomi masu rajin kare dimokradiyya na duniya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
‘Yan Majalisar Ghana Sun Gargadi Shugaban Kasar Kan Tura Sojoji Nijar

'Yan Majalisar Ghana Sun Gargadi Shugaban Kasar Kan Tura Sojoji Nijar

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.