• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojojin Nijar Za Su Mika Mulki Nan Da Shekara 3 – Janar Tchiani

by Sadiq
2 years ago
in Da ɗumi-ɗuminsa, Kasashen Ketare, Manyan Labarai
0
Sojojin Nijar Za Su Mika Mulki Nan Da Shekara 3 – Janar Tchiani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Janar Tchiani ya ce nan da wata daya za su kafa kwamitin da zai yi nazari kan sabon kundin tsarin mulki na kasar.

Shugaban sojojin da suka yi juyin mulki a Jamhuriyar Nijar Janar Abdourahamane Tchiani ya ce za su mika mulki ga gwamnatin farar-hula nan da shekaru uku masu zuwa.

  • Zantawa Da Dilma Rousseff, Shugabar Sabon Bankin Samar Da Ci Gaba
  • Kwamandojin Boko Haram 4 Da Wasu 13 Sun Mika Wuya Ga MNJTF

Ya bayyana haka ne a jawabin da ya gabatar ta gidan talabijin na kasar ranar Asabar da daddare.

Ya yi jawabin ne jim kadan bayan ya gana da tawagar kungiyar ECOWAS, karkashin jagorancin tsohon shugaban Nijeriya Janar Abdulsalami Abubakar.

Janar Tchiani ya ce nan da wata daya za su kafa kwamitin da zai yi nazari kan sabon kundin tsarin mulki na kasar.

Labarai Masu Nasaba

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Ya kara da cewa Nijar ba ta son zuwa yaki kuma kofarsu a bude take su tattauna, amma kuma za su kare kansu idan bukatar hakan ta taso.

A gefe guda, tawagar Kungiyar ECOWAS karkashin jagorancin tsohon shugaban Nijeriya Janar Abdulsalami Abubakar ta gana da hambararren shugaban Nijar Mohamed Bazoum a Yamai, babban birnin kasar ranar Asabar.

Tawagar ta je Yamai ne domin lalubo hanyar magance rikicin siyasar da kasar ta fada a ciki tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi wa Bazoum ranar 26 ga watan Yuli.

Janar Abubakar ya shaida wa manema labarai cewa tawagarsa ta saurari bayani daga wurin Bazoum da kuma kalubalen da yake fuskanta tun da aka kifar da gwamnatinsa.

“Mun gan shi mun ji nashi ra’ayin da abin da aka yi mashi. Kuma akwai wasu ‘yan matsaloli wadanda ke tare da shi da ya yi mana bayani wadanda za mu gaya wa shugabanninmu,” in ji shi.

Ko da yake bai yi karin bayani game da ganawar ba, amma ya ce “wannan taro da aka yi Allah ya sa an samu mabudi ke nan da za mu ci gaba da tattaunawa don a samu a warware wannan matsala.”

Tun da fari Firaiministan kasar Ali Mahamane Laminé Zeine ya tarbi tawagar a filin jirgin sama na Diori Hamani.

Wannan tattaunawar na zuwa ne kwana guda bayan hafsoshin tsaron kasashen ECOWAS sun kammala taronsu a Ghana inda suka saka ranar da za su tura dakarunsu Jamhuriyyar Nijar idan hanyoyin diflomasiyya suka ci tura.

Wannan ne karo na biyu da wakilan ECOWAS karkashin jagorancin Abdulsalami Abubakar da Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar ke zuwa Nijar domin sulhu.

A karon farko ba su samu ganawa da Janar Abdourahamane Tchiani ba inda suka koma ba tare da an cimma wata matsaya ba.

A ranar Juma’a ne kasashen Mali da Burkina Faso suka aike da jiragen yaki Nijar domin tallafa wa sojojin kasar kan duk wata barazana da za su fuskanta daga dakarun ECOWAS.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BazoumECOWASJuyin MulkiNijarSojoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Zantawa Da Dilma Rousseff, Shugabar Sabon Bankin Samar Da Ci Gaba

Next Post

Gwamnan Katsina Ya Nuna Takaicinsa Kan ‘Yan Kasuwar Da Ke Boye Abinci 

Related

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

1 hour ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

2 hours ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

10 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

14 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

15 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

17 hours ago
Next Post
Gwamnan Katsina Ya Nuna Takaicinsa Kan ‘Yan Kasuwar Da Ke Boye Abinci 

Gwamnan Katsina Ya Nuna Takaicinsa Kan ‘Yan Kasuwar Da Ke Boye Abinci 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.