ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 19, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojojin Nijar Za Su Mika Mulki Nan Da Shekara 3 – Janar Tchiani

by Sadiq
3 years ago
Nijar

Janar Tchiani ya ce nan da wata daya za su kafa kwamitin da zai yi nazari kan sabon kundin tsarin mulki na kasar.

Shugaban sojojin da suka yi juyin mulki a Jamhuriyar Nijar Janar Abdourahamane Tchiani ya ce za su mika mulki ga gwamnatin farar-hula nan da shekaru uku masu zuwa.

  • Zantawa Da Dilma Rousseff, Shugabar Sabon Bankin Samar Da Ci Gaba
  • Kwamandojin Boko Haram 4 Da Wasu 13 Sun Mika Wuya Ga MNJTF

Ya bayyana haka ne a jawabin da ya gabatar ta gidan talabijin na kasar ranar Asabar da daddare.

ADVERTISEMENT

Ya yi jawabin ne jim kadan bayan ya gana da tawagar kungiyar ECOWAS, karkashin jagorancin tsohon shugaban Nijeriya Janar Abdulsalami Abubakar.

Janar Tchiani ya ce nan da wata daya za su kafa kwamitin da zai yi nazari kan sabon kundin tsarin mulki na kasar.

LABARAI MASU NASABA

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

Ya kara da cewa Nijar ba ta son zuwa yaki kuma kofarsu a bude take su tattauna, amma kuma za su kare kansu idan bukatar hakan ta taso.

A gefe guda, tawagar Kungiyar ECOWAS karkashin jagorancin tsohon shugaban Nijeriya Janar Abdulsalami Abubakar ta gana da hambararren shugaban Nijar Mohamed Bazoum a Yamai, babban birnin kasar ranar Asabar.

Tawagar ta je Yamai ne domin lalubo hanyar magance rikicin siyasar da kasar ta fada a ciki tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi wa Bazoum ranar 26 ga watan Yuli.

Janar Abubakar ya shaida wa manema labarai cewa tawagarsa ta saurari bayani daga wurin Bazoum da kuma kalubalen da yake fuskanta tun da aka kifar da gwamnatinsa.

“Mun gan shi mun ji nashi ra’ayin da abin da aka yi mashi. Kuma akwai wasu ‘yan matsaloli wadanda ke tare da shi da ya yi mana bayani wadanda za mu gaya wa shugabanninmu,” in ji shi.

Ko da yake bai yi karin bayani game da ganawar ba, amma ya ce “wannan taro da aka yi Allah ya sa an samu mabudi ke nan da za mu ci gaba da tattaunawa don a samu a warware wannan matsala.”

Tun da fari Firaiministan kasar Ali Mahamane Laminé Zeine ya tarbi tawagar a filin jirgin sama na Diori Hamani.

Wannan tattaunawar na zuwa ne kwana guda bayan hafsoshin tsaron kasashen ECOWAS sun kammala taronsu a Ghana inda suka saka ranar da za su tura dakarunsu Jamhuriyyar Nijar idan hanyoyin diflomasiyya suka ci tura.

Wannan ne karo na biyu da wakilan ECOWAS karkashin jagorancin Abdulsalami Abubakar da Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar ke zuwa Nijar domin sulhu.

A karon farko ba su samu ganawa da Janar Abdourahamane Tchiani ba inda suka koma ba tare da an cimma wata matsaya ba.

A ranar Juma’a ne kasashen Mali da Burkina Faso suka aike da jiragen yaki Nijar domin tallafa wa sojojin kasar kan duk wata barazana da za su fuskanta daga dakarun ECOWAS.

MASU ALAKA

majalisar kasa
Manyan Labarai

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya
Wasanni

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026
Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna
Rahotonni

Yadda Gano Ma’adanin ‘Lithium’ Zai Sauya Rayuwar Al’ummar Kudancin Kaduna

July 18, 2026
Next Post
Gwamnan Katsina Ya Nuna Takaicinsa Kan ‘Yan Kasuwar Da Ke Boye Abinci 

Gwamnan Katsina Ya Nuna Takaicinsa Kan ‘Yan Kasuwar Da Ke Boye Abinci 

LABARAI MASU NASABA

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

July 19, 2026
majalisar kasa

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026
Nijar

Abubuwa Shida Da Ya Kamata Mace Ta Sani Kafin Ta Yi Aure

July 19, 2026
An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

An Kaddamar Da “Bikin Fasahar AI Na Sin Na 2026” A Shanghai

July 18, 2026
Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

Fim Ko Gaske:Yaushe Masu Kallon Fina-finai Za Su Daina Daukar Fim A Matsayin Gaske

July 18, 2026
Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

Sin Ta Nuna Matukar Adawa Da Matakin Burtaniya Na Mallake Kamfanin Karafa Na British Steel

July 18, 2026
Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

Tasirin AI (Artificial Intelligence) A Harkokin Al’umma Na Yau Da Kullum

July 18, 2026
Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

Xavi Ya Ce A Shirye Yake Ya Karɓi Ragamar Horar Da Tawagar Ƙasa

July 18, 2026
Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

Masanin Kimiyya Na Sin Ya Lashe Kyautar UNESCO-Russia Mendeleev A Fannin Tushen Kimiyya

July 18, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.