• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rage Radadi: Gwamnatin Gombe Ta Amince Da Karin Albashin N10, 000 Ga Kowani Ma’aikaci

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Gwamnatin Gombe

Gwamnatin Jihar Gombe ta sanar da yin karin albashin naira dubu goma-goma (N10,000) ga kowani ma’aikacin gwamnati a fadin jihar domin rage radadi da matsatsin cire tallafin Mai.

Da ya ke ganawa da ‘yan jarida a Gombe ranar Juma’a, mataimain gwamnan jihar, Dakta Manassah Daniel Jatau, ya ce, wannan wani bari ne na cikin matakan da gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ke dauka na rage wa ma’aikata matsatsin tattalin arziki da ake ciki sakamakon cire tallafin na mai.

  • Cire Tallafi: Gwamnan Gombe Ya Raba Kayayyakin Abinci Da Kayan Noma Ga Mutane 450,000

Ya ce, gwamna Inuwa Yahaya ya maida hankali sosai kan tabbatar da walwala da jin dadin ma’aikata tare da al’ummar jihar ta hanyar shirye-shirye masu dama kuma masu fa’ida tun lokacin barkewar annobar Korana.

Ya kara da cewa tun lokacin da aka zare tallafin mai, gwamnatin jihar take ta daukan matakai da bijiro da tsare-tsaren da za su taimaka wa jama’a wajen rage musu kaifin matsatsi da shiga takura a sakamakon hakan.

Ya kara da cewa, daga cikin matakan da gwamnatin ta dauka har da raba tallafin naira dubu talatin-talatin (N30,000) wa mutum 420 000 a sassan jihar.

LABARAI MASU NASABA

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

A fadin nasa, wannan karin albashin dubu 10 zai shafi dukkanin ma’aikatan gwamnati na jiha da na kananan hukumomi kuma zai fara aiki ne daga watan Agustan 2023.

Da aka tambayeshi kan zuwa yaushe ne karin zai tsaya, sai ya ce, “Karin dubu 10 kan albashin ma’aikatan babu ranar tsaida shi a yanzu.”

Mataimakin gwamnan ya jinjina ya gudunmawar da ma’aikatan jihar ke bayarwa, ya misaltasu a matsayin injunan da suke taimaka wa gwamnati wajen tafiyar da shirye-shirye da manufofinta.

Jatau ya kuma roki ma’aikatan jihar da su cigaba da kasancewa masu biyayya wa doka da oda, kuma ya roki wadanda har zuwa yanzu ba su samu tallafi ba da cewa su kara hakuri kaso na zuwa kansu.

“Ina kira ga al’umma musamman wadanda har yanzu ba su samu tallafi ba da su kara hakuri, a bangarenmu za mu cigaba da kawo tsare-tsare da kusan kowa sai ya mora da dan abun da muke da shi a hannu,” ya tabbatar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Labarai

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI
Manyan Labarai

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
Next Post
An Kaddamar Da Shirin Baje Kolin Inganta Harkar Noma Da Sana’o’i A Kano

An Kaddamar Da Shirin Baje Kolin Inganta Harkar Noma Da Sana'o’i A Kano

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.