ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cire Tallafi: Gwamnan Gombe Ya Raba Kayayyakin Abinci Da Kayan Noma Ga Mutane 450,000

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gombe

Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya ya kaddamar da rabon kayan abinci da kayan noma don rage matsalolin tattalin arziki da ake fuskanta sakamakon cire tallafin man fetur ga al’ummar jihar. 

 

Da ya ke jawabi a waje bikin rabon kayayyakin wadda aka gudanar a fadar Sarkin Yamaltu da ke Dadinkowa jiya, Gwamnan ya bayyana cewa kaddamar da rabon kayan tallafin wani gagarumin kokari ne na tallafawa fiye da mutane 450,000 da za su ci gajiya a fadin kananan hukumomi 11 na jihar.

ADVERTISEMENT
  • Lalacewar Hanyar Bauchi Zuwa Gombe Ta Zama Tarkon Mutuwa Ga Matafiya – Gwamna Inuwa

“A kashi na farko da muka kaddamar a yau, za mu tallafawa mutane dubu 30,000 ne inda kowane mutum zai samu buhun shinkafa mai girman Kilogram biyar da katon din macaroni daya da buhunan taki biyu da lita biyu na maganin kashe kwari”.

 

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

“Abin da ya sa wannan shiri ya sha bambam da sauran shirye-shirye shi ne dabarar sanya kayan noma a cikin rabon kayan abinci, wannan shawarar tana da matukar tasiri duba da yadda kaso mai tsoka na al’ummar Jihar Gombe sun dogara ne da noma don gudanar da harkokin rayuwarsu.”

Gombe

A cewarsa, ba da tallafin noman zai taimaka matuka wajen samar da isasshen abinci a lokacin kaka.

 

Da yake bayyana wajibcin cire tallafin man fetur, Gwamna Inuwa ya ce hakan wani mataki ne na tabbatar da dorewar tattalin arziki da ci gaba. Ya kara da cewa, an tsara tallafin ne bayan fahimtar irin kalubale daban-daban da magidanta ke fuskanta a Jihar Gombe sakamakon tabarbarewar tattalin arziki.

 

Baya ga rabon kayayyakin, Gwamna Inuwa ya ce, shirin tallafin yana kuma nuna tausayi da jajircewarsa ga jin dadin kowane dan Jihar Gombe.

 

Don haka ya bukaci al’ummar jihar su sanya dabi’un tausayi da hadin kai a cikin mu’amalarsu, tare da tallafawa mabukata.

 

Gwamnan ya yi kira ga jami’an rabon kayayyakin da ‘yan sa kai su gudanar da ayyukansu cikin gaskiya da rikon amana don tabbatar da gaskiya da adalci.

Gombe

Gwamna Inuwa Yahaya ya tabbatarwa jama’a cewa gwamnatin sa tana kokarin ƙara samar da ayyukan yi ga al’umma don bunkasar harkokin ci gaba, da dakile kalubalen tattalin arzikin da jama’a ke fuskanta.

 

Shugaban kwamitin kula da rabon kayan abinci na jiha Abdullahi Haruna Abdullahi, ya tabbatarwa Gwamnan cewa kwamitin zai gudanar da aikinsa cikin tsantseni da tsoron Allah don amfanar al’umma.

 

Abdullahi wanda kuma shi ne Sakataren zartarwa na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Gombe SEMA, ya bayyana cewa an kafa wasu kananan kwamitoci a matakin kananan hukumomi da gundumomi don tabbatar da cewa kayayyakin sun kai ga marasa galihu a jihar.

Gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Next Post
Xi Jinping Zai Halarci Taron Ganawar Shugabannin Kasashen BRICS Karo Na 15

Xi Jinping Zai Halarci Taron Ganawar Shugabannin Kasashen BRICS Karo Na 15

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.