ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kaddamar Da Shirin Baje Kolin Inganta Harkar Noma Da Sana’o’i A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
Noma

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

An bayyana shirin Gwamnati Na Kano CARRES da cewa shi ne shirin da yafi sauran shirye shiryen da ake bijiro dasu da sunan tallafin saukakawa jama’a radadin matsin rayuwa da jama’a ke fama da ita tun bayan faruwar Annobar Korona wadda tayi sanadin durkushewar tatalin jama’a.

Shugaban Hukumar Kano CARES na Jihar Kano Alhaji Rufa’I ne yabayyana haka alokacin da yake zagawa da babban sakataren ma’aikatar gona na Jihar Kano Alhaji Salisu Tahir alokacin shirin da ake na kaddamar da tallafin kayan Noma ga daruruwan matasa maza da mata a Jihar Kano.

  • Tinubu Ya Kori Shugaban Hukumar NASENI Bayan Wata 3 Da Nadinsa
  • Rage Radadin Cire Tallafi: Gwamnati Ta Baiwa  Kowacce Jiha Naira Biliyan Biyu A Kashin Farko

Alhaji Rufa’I ya shaidawa Babban sakataren Ma’aikatar gonan na jIhar Kano cewar wannan hukuma ta himmatu kamar yadda aka bata cikin kudin tsare tsaren wannan hukuma na samar da tallafi kamar bayar da injunan nika, injin malkade, injin ban ruwa mai amfani da hasken rana, kiwon Kaji, samar da hanyoyi a karkara da kuma gina wuraren kewayawa a kasuwanni da wuraren taruwar al’umma.

Hakazalika shugaban hukumar ta Kano CARES  ya bayyanawa mahalarta taron irin yadda majalisar mahaddata alkur’ani suma suka shigo cikin tsarin, musamman ganin suna da kyakkyawan shirin rage kwararar almajirai daga kauyuka zuwa manyan birane tare da kokarin magance matsalar barace barace wadda a halin ke neman zama wata barazana a jihar Kano, don haka sai ya tabbatar da cewa yanzu haka shirye shirye sunyi nisa na sake samar da wani rukunin al’umma da suma ake fatan zasu rabauta da wannan tallafi da Gwamnatin Kano ke saukewa al’ummarta.

Da yake jawabi alokacin da yake ganewa idonsa irin kayayyakin da hukumar ta samar domin rabawa al’umma musamman abinda ya shafi noma, kiwo da sana’o’in dogaro da kai, Dakta Farouk Kurawa ya bayyana farin cikinsa tare da jinjinawa kokarin wannan hukuma wadda yace babu shakka ya fahimci yadda jama’a ke alfahari da ayyukan wannan hukuma ke nuni da kyakkyawan alhairan da ke kunshe cikin manufofi da aikace aikacen hukumar ta Kano CARES.

Shima da yake duba kayayyakin da hukumar Kano CARES ta tanada domin ci gaba da rabawa jama’a, babban sakataren ma’aikatar gona na Jihar Kano Alhaji Salisu Tahir ya nuna gamsuwa da irin kalaman da yaji daga bakin wadanda suka amfana da alhairan wannan hukuma ta Kano CARES, musamman kan batan smaar da hanyoyi a karkara, inda wasu da suka amfana daga Kananan Hukumomi Gazawa da Kura suka bayyana farin cikin al’umarsu bis aaikin hanya da wannan hukuma ta shimfada masu a yankunansu.

Alhaji Salisu Tahir ya jinjinawa kokarin shugabannin hukuma tare da rokonsu da su kara himma wajen sauke nauyin da aka dora masu, sannan kuma ya bukaci wadanda suka amfana da wadanann tallafi iri daban daban da suyi kyakkyawan amfani dashi, domin ganin nan gaba kadan suma sun zama suna cikin wadanda da za su taimaka wa sauran al’umma. A karshe ya yi addu’ar Allah ya sawa damunar mu albarka.

Noma
Abdullahi Muh'd Sheka
+ postsBio
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Sakamakon Matsin Lambar Jami’an Tsaro, ‘Yan Ta’adda Na Fuskantar Ƙarancin Abinci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Kisan Gillar Mutum 7 A Kano: Sarakuna Da Malamai Da Iyaye Sun Nemi A Gaggauta Yanke Wa Waɗanda Ake Zargi Hukunci
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi
  • Abdullahi Muh'd Sheka
    https://hausa.leadership.ng/author/abdullahi-muhd-sheka/
    Faɗace-Faɗacen Daba Da Ƙwacen Waya A Kano Ya Ɗauki Sabon Salo
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Gwamnan Kaduna

Gwamnan Kaduna Ya Bude Masaukin Dalibai Mai Gado 400 Da Ofishin Hukumar Raya Birnin Zariya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.