• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

SERAP Ta Maka Tinubu A Kotu Kan Haramta Wa ‘Yan Jarida 25 Dauko Rahotonni A Fadar Shugaban Kasa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Serap
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata kungiya mai fafukatar yaki da cin hanci a Nijeriya (SERAP) ta maka gwamnatin shugahan kasa Bola Ahmed Tinubu a kotu bisa abin da ta kira “Haramtaccen hanawa da dakatar da ‘yan jarida 25 da aka tantance daukowa da yada labarai daga fadar shugahan kasa.”

A cewar rahotonni, gwamnatin tarayya a ranar 18 ga watan Agustan 2023 ta janye izinin tantancewa da sahalewar ‘tags’ da ke bai wa ‘yan jarida 25 da gidajen yada labarai damar shiga fadar shugaban kasa domin dauko rahotonnin abubuwan da ke faruwa a fadar shugaban kasa, Abuja.

  • Gwamnatin Zamfara Ta Rufe Wasu Kasuwannin Shanu A Jihar

An shaida wa ‘yan jaridan da lamarin ya shafa da su mika shaidar izinin shiga da aka basu ‘tags’ a mashigar babbar kofar fadar shugaban kasa.

Sai dai, SERAP ta ce haramcin ya saba da doka kuma bai dace ba kwata-kwata.

A kara mai lambar alama (FHC/L/CS/1766/23) da SERAP ta shigar a gaban babban kotun tarayya da ke Legas, ta roki, “Kotu da ta bada umarni da tilasta wa shugaban kasa Bola Tinubu janye haramta wa ‘yan jarida 25 da gidajen watsa labarai daga dauka da yada harkokin da suke faruwa a Villa.”

Labarai Masu Nasaba

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Kazalika, SERAP ta roki kotun da ta hana shugaba Tinubu, kowace hukuma, wani ko wasu daga janye izinin shiga fadar shugaban kasa ga ‘yan jarida masu farauto labarai ba tare da dalili na doka ba domin kauce wa tauye hakkin fadin albarkacin baki, take hakkin samun bayanai da kuma tauye wa gidajen jaridu hakkinsu.

A cewar SERAP idan har ba a tilasta wa gwamnatin janye wannan matakin nata ba, akwai yiyuwar hakan ya bude ma wasu dama su dukufa tauye hakkin samun bayanai, kasancewa cikin lamura da ‘yancin gidajen yada labarai.

Lauyoyi Ebun-Olu Adegboruwa (SAN), Kolawole Oluwadare, da Ms Valentina Adegoke, su ne suka shigar da karar a madadin SERAP, kungiyar ta ce, ‘yan jarida na taka muhimmiyar rawa don haka da bukatar su samu cikakken damar samun bayanai domin kyautata demukuradiya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Fadar Shugaban KasaVilla
ShareTweetSendShare
Previous Post

Menene Sabon Karfin Ingizawa Zai Kawowa Duniya

Next Post

Ronaldo Ya Ci Kwallo Ta 850 A Tarihin Kwallonsa

Related

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

11 minutes ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

41 minutes ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

1 hour ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

2 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

3 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

5 hours ago
Next Post
Ronaldo Ya Ci Kwallo Ta 850 A Tarihin Kwallonsa

Ronaldo Ya Ci Kwallo Ta 850 A Tarihin Kwallonsa

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.