• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manyan Kasashen Duniya Na Neman Cin Gajiyar Ci Gaban Kasar Sin

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A farkon wannan mako ne ministan harkokin wajen kasar Italiya Antonio Tajani ya fara ziyara a kasar Sin. Ziyarar da ta zo a daidai lokacin da ake ta tsokaci game da kasancewar kasar cikin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, kasancewarta kasar Turai tilo dake cikin shawarar.

Yayin da shawarar Ziri Daya da Hanya Daya ke cika shekaru 10, kasar Italiya ta kasance cikin wadanda suka ci gajiyarta. Misali kadan daga ciki ya hada da yadda yawan cinikayya tsakanin kasashen biyu ya habaka zuwa kusan dala biliyan 80 daga dala biliyan 50.

  • Kamfanin Makamashi Na Sin Ya Cimma Gagarumar Nasara A Fannin Karfin Wutar Lantarki Da Ake Iya Sabuntawa

Haka kuma yawan kayayyakin da Italiya ke shigo da su kasar Sin ya karu da kaso 30 cikin shekaru 5 da suka gabata. Wannan kadai ya nuna yadda Sin take taka gagarumar rawa wajen bunkasa cinikayya da ma tattalin arzikin kasar ta Turai. Haka zalika, ya nuna cewa, duk da yunkurin da wasu kasashen yamma ke yi na neman raba gari da Sin ko rage dogaro da ita, ra’ayin wasu da dama ya bambanta, kuma sun san abun da kasashensu da duniya ke bukata domin samun ci gaba a wannan zamani da ake fuskantar kalubale. Za mu iya gane hakan idan muka yi la’akari da cewa, Antonio Tajani shi ne babban jami’i na 4 daga kasashen kungiyar G7 da ya kawo ziyara Sin a baya-bayan nan.

Irin wannan ziyara da manyan jami’an manyan kasashe ke kawowa kasar Sin, yana kara bayyanawa al’ummar duniya cewa, jita-jitar da ake yadawa ba su da kamshin gaskiya ko kadan, kana ana yinsu ne da zummar bata sunan kasar Sin da kuma kokarin dakile ci gabanta, ganin irin tagomashin da take samu a duniya da ma jajircewarta wajen raya kanta bisa tsayawa da kafarta.

A yayin tattaunawarsa da ’yan kasuwar kasarsa dake Sin, Tajani ya ce gwamnatinsu na son inganta musu hanyoyin kara shiga kasuwar kasar Sin. Abun nufi, gwamnatin kasarsa na son kara cin gajiyar kasar Sin da ma dimbin damarmakin kasuwanci da bude kofar da take kara yi ga ’yan kasuwa da masu zuba jari na kasashen ketare. Lamarin dake kara jaddada cewa, raba gari da kasar Sin ba abu ne mai yiwuwa ba. Kana su ma manyan kasashen duniya, suna son cin gajiyar ci gaban kasar Sin da dimbin damarmakin da take da su.

Labarai Masu Nasaba

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Ita dai Sin ta sha nanata cewa, a shirye take ta yayata fasahohinta tare da ba kasashen duniya damar cin gajiyar ci gabanta da tafarkin da ta dauka na zamanintar da kanta. (Faeza Mustapha)

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

DA DUMI DUMINSA: Kotu Ta Dakatar Da Korar Kwankwaso Daga Jam’iyyar NNPP

Next Post

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabar Kwamitin Kasa Da Kasa Na Red Cross

Related

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

19 hours ago
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

20 hours ago
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12
Daga Birnin Sin

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

21 hours ago
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana
Daga Birnin Sin

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

22 hours ago
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

23 hours ago
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa
Daga Birnin Sin

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

24 hours ago
Next Post
Red Cross

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabar Kwamitin Kasa Da Kasa Na Red Cross

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.