• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaddamar Zaben Gwamnan Jihar Kaduna…

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Takaddamar Zaben Gwamnan Jihar Kaduna…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bayyana cewa shaidun babbar jam’iyyar adawa ta PDP da ke kalubalantar lashe zabensa ne suka tabbatar masa da nasara cikin rashin sani.

Ya bayyana hakan ne a jawabinsa na karshe ga kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan Kaduna, wanda tawagar lauyoyinsa karkashin jagorancin tsohon babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a, Cif Bayo Ojo suka bayyana.

  • Hukuncin Kotun Zabe: Martanin Da Atiku Da Obi Suka Mayar Kan Tabbatar Da Nasarar Tinubu
  • Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Jam’iyyar APM Ta Shigar Kan Ingancin Shettima

Babbar Jam’iyyar adawa ta kalubalanci ayyana Uba Sani a matsayin wanda ya lashe zaben da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta gudanar tare da dan takararta Mohammed Ashiru Isa, suna neman a sake sakamakon zabe.

A cikin karar da ake kalubalantar nasarar Uba Sani, masu shigar da kara sun kira shaidu 24 tare da gabatar da su a gaban kotu.

A ranar Litinin 4 ga watan Satumba, kotun sauraron karar zaben gwamnan Jihar Kaduna ta kammala amsar dukkanin shaidun da aka gabatar mata, wanda a yanzu ana jiran yanke hukunci ne kawai.

Labarai Masu Nasaba

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

A cewar gwamnan, masu shigar da kara sun taimaka masa wajen tabbatar da nasararsa ta lashe zaben gwamnan Jihar Kaduna, inda suka yi nuni da karbi shaida daga, Bonett Gwazah, wani babban manazarcin sashen sadarwa a hukumar INEC na Jihar Kaduna.

Gwamnan ta bakin lauyansa ya ce, “Masu shigar da karar sun kira jimillar shaidu 24, wadanda akasarin bayanansu na rantsuwar an gabatar da su ne bisa sammacin da aka bayar a lokacin da ake sauraron karar.

“Bayan an rufe amsar shaidu, wanda ake kara bai da wata bukata ta kira shaidu, bayan da suka fitar da isassun shaidu a karkashin binciken da aka gudanar, wanda shaidun sun goyi bayan bangaren da ake kara”.

Kotun sauraron karar da ke karkashin mai ahari’a, Bictor Obiawie, ta yi alkawarin a kowane lokaci za ta yanke hukunc a nan gaba bisa adalci ga kowani bangare.

Ita ma hukumar zaben wadda ita ce farkon wacce aka shigar da koken a kanta, ta tabo batun wani kuskuren da masu shigar da kara suka yi kan amincewa da takardun zabe.

A halin da ake ciki kuma, dan takarar gwamnan Jihar Kaduna a karkashin jam’iyyar PDP a zaben da ya gudana a ranar 18 ga Maris, 2023, Hon. Isa Ashiru, ya bayyana cewa sakamakon zabe guda biyu masu cin karo da juna da suka fito daga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a Jihar Kaduna, wanda a cewarsa, ya hana shi samun nasara a zaben.

Dan takarar gwamnan na PDP ya bayyana haka ne a gaban kotun sauraron karar zaben gwamnan Jihar Kaduna, inda ya kara jaddada cewa INEC ta sauya sakamakon zaben na asali domin bai wa jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Bayan gabatar da jawabinsa na karshe a rubuce a gaban alkalan kotun mai mutum 3 karkashin jagorancin Bictor Obiawie, Ashiru ta bakin babban lauyansa, Oluwole Iyamu ya bayyana cewa INEC ce ta sauya sakamakon zaben.

Ashiru ya kuma yi zargin cewa an samu kuri’u da suka wuce ka’ida da kuma kin bin tsarin zabe, yayin da ya yi kira da INEC kar ta bayyana sunan Uba Sani a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan Jihar Kaduna.

A halin yanzu dai, bayan karbar hujjoji na karshe daga kowani bangare, kotun ta dage yanke hukunci har zuwa wata rana da za ta sanar da lauyoyin nan gaba.

A yanzu haka dai ana dakon yanke hukunci na karshe.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yanke Hukunci: Abubuwan Da Suka Ja Hankali A Kotun Zaben Shugaban Kasa

Next Post

Xi Ya Jaddada Bude Wani Sabon Babi Na Ci Gaban Heilongjiang Mai Inganci

Related

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben Cike Gurbi: Tinubu Ya Lalata Tsarin Zaben Nijeriya — ADC

4 days ago
An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Rarrabuwar Kawuna A Jam’iyyar ADC Kan Shugabancin David Mark

2 weeks ago
Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa
Tambarin Dimokuradiyya

Muhimman Batutuwan Da Za Mu Yi La’akari Da Su Kafin Amincewa Da Bukatun Kirkirar Sabbin Jihohi — Majalisar Dattawa

2 weeks ago
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?

1 month ago
Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 
Tambarin Dimokuradiyya

Dalilin Da Ya Sa Har Yanzu Obi Da El-Rufai Ba Su Shiga ADC A Hukumance Ba — Kakakin Jam’iyyar 

1 month ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku

1 month ago
Next Post
Heilongjiang

Xi Ya Jaddada Bude Wani Sabon Babi Na Ci Gaban Heilongjiang Mai Inganci

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hukumar NRC Ta Dakatar Da Zirga-zirgar Jiragen Kasa Na Abuja zuwa Kaduna

August 26, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

August 26, 2025
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

August 26, 2025
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutane 128 Daga Hannun ‘Yan Bindiga A Zamfara

August 26, 2025
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

August 26, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.