ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Takaddamar Zaben Gwamnan Jihar Kaduna…

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Kaduna

Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya bayyana cewa shaidun babbar jam’iyyar adawa ta PDP da ke kalubalantar lashe zabensa ne suka tabbatar masa da nasara cikin rashin sani.

Ya bayyana hakan ne a jawabinsa na karshe ga kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan Kaduna, wanda tawagar lauyoyinsa karkashin jagorancin tsohon babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a, Cif Bayo Ojo suka bayyana.

  • Hukuncin Kotun Zabe: Martanin Da Atiku Da Obi Suka Mayar Kan Tabbatar Da Nasarar Tinubu
  • Kotu Ta Yi Watsi Da Karar Da Jam’iyyar APM Ta Shigar Kan Ingancin Shettima

Babbar Jam’iyyar adawa ta kalubalanci ayyana Uba Sani a matsayin wanda ya lashe zaben da hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta gudanar tare da dan takararta Mohammed Ashiru Isa, suna neman a sake sakamakon zabe.

ADVERTISEMENT

A cikin karar da ake kalubalantar nasarar Uba Sani, masu shigar da kara sun kira shaidu 24 tare da gabatar da su a gaban kotu.

A ranar Litinin 4 ga watan Satumba, kotun sauraron karar zaben gwamnan Jihar Kaduna ta kammala amsar dukkanin shaidun da aka gabatar mata, wanda a yanzu ana jiran yanke hukunci ne kawai.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

A cewar gwamnan, masu shigar da kara sun taimaka masa wajen tabbatar da nasararsa ta lashe zaben gwamnan Jihar Kaduna, inda suka yi nuni da karbi shaida daga, Bonett Gwazah, wani babban manazarcin sashen sadarwa a hukumar INEC na Jihar Kaduna.

Gwamnan ta bakin lauyansa ya ce, “Masu shigar da karar sun kira jimillar shaidu 24, wadanda akasarin bayanansu na rantsuwar an gabatar da su ne bisa sammacin da aka bayar a lokacin da ake sauraron karar.

“Bayan an rufe amsar shaidu, wanda ake kara bai da wata bukata ta kira shaidu, bayan da suka fitar da isassun shaidu a karkashin binciken da aka gudanar, wanda shaidun sun goyi bayan bangaren da ake kara”.

Kotun sauraron karar da ke karkashin mai ahari’a, Bictor Obiawie, ta yi alkawarin a kowane lokaci za ta yanke hukunc a nan gaba bisa adalci ga kowani bangare.

Ita ma hukumar zaben wadda ita ce farkon wacce aka shigar da koken a kanta, ta tabo batun wani kuskuren da masu shigar da kara suka yi kan amincewa da takardun zabe.

A halin da ake ciki kuma, dan takarar gwamnan Jihar Kaduna a karkashin jam’iyyar PDP a zaben da ya gudana a ranar 18 ga Maris, 2023, Hon. Isa Ashiru, ya bayyana cewa sakamakon zabe guda biyu masu cin karo da juna da suka fito daga hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a Jihar Kaduna, wanda a cewarsa, ya hana shi samun nasara a zaben.

Dan takarar gwamnan na PDP ya bayyana haka ne a gaban kotun sauraron karar zaben gwamnan Jihar Kaduna, inda ya kara jaddada cewa INEC ta sauya sakamakon zaben na asali domin bai wa jam’iyyar APC mai mulki a jihar.

Bayan gabatar da jawabinsa na karshe a rubuce a gaban alkalan kotun mai mutum 3 karkashin jagorancin Bictor Obiawie, Ashiru ta bakin babban lauyansa, Oluwole Iyamu ya bayyana cewa INEC ce ta sauya sakamakon zaben.

Ashiru ya kuma yi zargin cewa an samu kuri’u da suka wuce ka’ida da kuma kin bin tsarin zabe, yayin da ya yi kira da INEC kar ta bayyana sunan Uba Sani a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan Jihar Kaduna.

A halin yanzu dai, bayan karbar hujjoji na karshe daga kowani bangare, kotun ta dage yanke hukunci har zuwa wata rana da za ta sanar da lauyoyin nan gaba.

A yanzu haka dai ana dakon yanke hukunci na karshe.

Kaduna
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Next Post
Heilongjiang

Xi Ya Jaddada Bude Wani Sabon Babi Na Ci Gaban Heilongjiang Mai Inganci

LABARAI MASU NASABA

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin  Mataimakinsa

M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa

July 16, 2026
Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

Saliba Zai Yi Jinyar Watanni 5 Bayan Raunin Da Ya Samu A Bayansa

July 16, 2026
Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.