ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Faransa Ta Aike Da Sojojinta Kasashen ECOWAS Don Shirin Kai Wa Nijar Hari

by Muhammad
2 years ago
Faransa

TRT ta rawaito cewa, Sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar a watan Yuli sun yi zargin cewa Faransa tana tura sojojinta zuwa kasashen Yammacin Afirka da dama da zummar yin amfani da “kafin soji” a kansu.

“Faransa tana ci gaba da kai dakarunta kasashen kungiyar ECOWAS da dama a wani bangare na shirin kaddamar da hare-hare kan Nijar, wanda take kitsawa tare da hadin gwiwar kungiyar,” a cewar kakakin sojojin Kanar Amadou Abdramane a wata sanarwar da ya karanta a gidan talabijin na kasar ranar Asabar da maraice.

  • Har Yanzu Jakadan Faransa Bai Fice Daga Jamhuriyar Nijar Ba – Macron
  • Juyin Mulki: Aljeriya Ta Bukaci Sojin Nijar Su Mika Mulki Cikin Watanni 6 Kacal

Ya ce Faransa ta tura dakarunta kasashen da suka hada da Senegal, Benin da Ivory Coast, a wani bangare na ”shirin kaddamar da hari” a kan Nijar.

ADVERTISEMENT

Kawo yanzu dai Faransa ba ta yi martani kan wanna zargi ba.

Amma Kanar Abdramane ya yi ikirarin cewa ranar 1 ga watan Satumba Faransa ta tura jiragen soji biyu da kuma wani jirgi samfurin Dornier 328 domin karfafa dakarunta da ke Ivory Coast, yayin da kuma ta tura jiragen helikwafta biyu samfurin PUMA da motoci masu silke 40 zuwa Benin.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

Ya kara da cewa ranar 7 ga watan Satumba wani jirgin ruwan yakin Faransa ya isa Cotonou babban birnin Benin dauke da dakaru.

Ranar Litinin Firaiministan Nijar Ali Mahaman Lamine Zeine ya ce sojojin suna tattaunawa da Faransa da zummar tabbatar da “gaggawar” kwashe dakarunta daga kasar.

Sai dai sojojin sun zargi Faransa da “rashin gaskiya da jan-kafa da kuma kafar-ungulu” don kawai ta kawar da su.

Dangantaka tsakanin Faransa da Nijar ta yi tsami bayan Paris ta dage cewa dole sojoji su mayar da hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum kan mulki bayan juyin mukin da suka yi masa ranar 26 ga watan Yuli.

Juyin mulkin ya sa kungiyar ECOWAS ta kakaba wa Nijar takunkumai sannan ta yi barazanar amfani da karfin soji idan aka gaza cimma matsayar mayar da Bazoum kan mulki ta hanyar diflomasiyya.

Faransa tana da dakaru sama da 1,500 a Nijar wadanda suke hadin-gwiwa wajen yaki da masu tayar da kayar baya a yankin Sahel, sai dai sojojin kasar sun soke dangantakar da ke tsakaninsu da kasar tun bayan juyin mulki.

Hasalima sun umarci jakadan Faransa ya fita daga Jamhuriyar Nijar, ko da yake har yanzu yana kasar.

Dubban mutane ne suka rika gudanar da zanga-zangar kin jinin Faransa a Yamai, inda suka bukaci kasar ta kwashe dakarunta daga Nijar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

December 22, 2025
Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

December 22, 2025
An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Next Post
AU Ta Zama Mamba Ta Dindindin A Kasashen G20 Masu Karfin Tattalin Arziki A Duniya

AU Ta Zama Mamba Ta Dindindin A Kasashen G20 Masu Karfin Tattalin Arziki A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

Gwamnatin Tarayya Ta Tabbatar Da Ceton Dukkan Ɗalibai 230 Da Aka Sace A Neja

December 22, 2025
Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

Gobara Ta Haddasa Mummunar Asara A Kasuwar Kayan Katako A Kano

December 22, 2025
An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.