• English
  • Business News
Monday, July 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Faransa Ta Aike Da Sojojinta Kasashen ECOWAS Don Shirin Kai Wa Nijar Hari

by Muhammad
2 years ago
in Labarai
0
Al’ummar Nijar Mazauna Kano Sun Yi Zanga-zanga Kan A Mayar Da Bazoum Bakin Aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

TRT ta rawaito cewa, Sojojin da suka yi juyin mulki a Nijar a watan Yuli sun yi zargin cewa Faransa tana tura sojojinta zuwa kasashen Yammacin Afirka da dama da zummar yin amfani da “kafin soji” a kansu.

“Faransa tana ci gaba da kai dakarunta kasashen kungiyar ECOWAS da dama a wani bangare na shirin kaddamar da hare-hare kan Nijar, wanda take kitsawa tare da hadin gwiwar kungiyar,” a cewar kakakin sojojin Kanar Amadou Abdramane a wata sanarwar da ya karanta a gidan talabijin na kasar ranar Asabar da maraice.

  • Har Yanzu Jakadan Faransa Bai Fice Daga Jamhuriyar Nijar Ba – Macron
  • Juyin Mulki: Aljeriya Ta Bukaci Sojin Nijar Su Mika Mulki Cikin Watanni 6 Kacal

Ya ce Faransa ta tura dakarunta kasashen da suka hada da Senegal, Benin da Ivory Coast, a wani bangare na ”shirin kaddamar da hari” a kan Nijar.

Kawo yanzu dai Faransa ba ta yi martani kan wanna zargi ba.

Amma Kanar Abdramane ya yi ikirarin cewa ranar 1 ga watan Satumba Faransa ta tura jiragen soji biyu da kuma wani jirgi samfurin Dornier 328 domin karfafa dakarunta da ke Ivory Coast, yayin da kuma ta tura jiragen helikwafta biyu samfurin PUMA da motoci masu silke 40 zuwa Benin.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Ya kara da cewa ranar 7 ga watan Satumba wani jirgin ruwan yakin Faransa ya isa Cotonou babban birnin Benin dauke da dakaru.

Ranar Litinin Firaiministan Nijar Ali Mahaman Lamine Zeine ya ce sojojin suna tattaunawa da Faransa da zummar tabbatar da “gaggawar” kwashe dakarunta daga kasar.

Sai dai sojojin sun zargi Faransa da “rashin gaskiya da jan-kafa da kuma kafar-ungulu” don kawai ta kawar da su.

Dangantaka tsakanin Faransa da Nijar ta yi tsami bayan Paris ta dage cewa dole sojoji su mayar da hambararren shugaban kasar Mohamed Bazoum kan mulki bayan juyin mukin da suka yi masa ranar 26 ga watan Yuli.

Juyin mulkin ya sa kungiyar ECOWAS ta kakaba wa Nijar takunkumai sannan ta yi barazanar amfani da karfin soji idan aka gaza cimma matsayar mayar da Bazoum kan mulki ta hanyar diflomasiyya.

Faransa tana da dakaru sama da 1,500 a Nijar wadanda suke hadin-gwiwa wajen yaki da masu tayar da kayar baya a yankin Sahel, sai dai sojojin kasar sun soke dangantakar da ke tsakaninsu da kasar tun bayan juyin mulki.

Hasalima sun umarci jakadan Faransa ya fita daga Jamhuriyar Nijar, ko da yake har yanzu yana kasar.

Dubban mutane ne suka rika gudanar da zanga-zangar kin jinin Faransa a Yamai, inda suka bukaci kasar ta kwashe dakarunta daga Nijar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FaransaNijar
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutum 15 Sun Rasu, 8 Sun Bace A Hatsarin Kwale-Kwale A Adamawa

Next Post

AU Ta Zama Mamba Ta Dindindin A Kasashen G20 Masu Karfin Tattalin Arziki A Duniya

Related

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

44 minutes ago
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari
Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

2 hours ago
Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami
Labarai

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

3 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni
Tsaro

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

4 hours ago
Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari
Manyan Labarai

Gwamnati Ta Kafa Kwamitin Tsara Yadda Za A Binne Buhari

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Talata A Matsayin Hutu Don Alhinin Marigayi Buhari

5 hours ago
Next Post
AU Ta Zama Mamba Ta Dindindin A Kasashen G20 Masu Karfin Tattalin Arziki A Duniya

AU Ta Zama Mamba Ta Dindindin A Kasashen G20 Masu Karfin Tattalin Arziki A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

Dangote Na Neman Izinin Gina Babbar Tashar Jiragen Ruwa Mafi Zurfi A Nijeriya

July 14, 2025
Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

Sin Da Amurka Na Kokarin Tabbatar Da Ci Gaban Da Aka Samu Na Yarjejeniyar London

July 14, 2025
Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

Sarkin Maroko Ya Aike Da Ta’aziyya Ga Nijeriya Bisa Rasuwar Buhari

July 14, 2025
Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

Sin Na Maraba Da ’Yan Jaridar Duniya Da Su Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Harin Japan Da Na Tafarkin Murdiya 

July 14, 2025
Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Osimhen Na Dab Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 14, 2025
Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

Gwamnan Zamfara Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Muhammadu Buhari

July 14, 2025
Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

Za A Iya Yarda Da Buhari Kan Kowace Irin Amana A Duniya — Abdulsalami

July 14, 2025
Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

Cinikayyar Shige Da Fice Ta Sin Ta Karu Da Kaso 2.9 Bisa Dari A Watanni Shida Na Farkon Bana

July 14, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 1,111, Sun Yi Garkuwa Da 276 A Nijeriya Cikin Watan Yuni

July 14, 2025
Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari

Kasar Sin Ta Nuna Alhinin Rasuwar Tsohon Shugaban Nijeriya Buhari

July 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.