• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 151, Sun Kama 456, Sun Kubutar Da 67

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Sojoji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hedikwatar Hukumar Tsaro ta kasa (DHQ) a ranar Alhamis ta ce, dakarun sojoji da aka tura aiki sassan kasar nan, sun samu nasarar hallaka ‘yan ta’adda 151 tare da ceto mutanen da aka yi garkuwa da su 76, kuma sun cafko ‘yan ta’adda 456 a sameme daban-daban da suka aiwatar a cikin mako guda tak.

Daraktan sashin yada labarai na hukumar tsaron, Manjo Janar Edward Buba, shi ne ya sanar da hakan yayin da ya ke ganawa da manema labarai kan ayyukan da sojojin suka aiwatar, inda ya ce, wasu mutum 45 da ake zargin barayin Danyen Man fetur ne, su ma an kamasu yayin da kuma aka kwato mai da darajarsa ya kai Naira Biliyan N1,011,851,250 da suka sace.

  • Sojoji Sun Ceto Mutum 18 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Arewa Maso Yamma

Ya ce, sojojin sun kuma kwato makamai daban-daban har guda 216 da alburusai 443.

Da yake jero makamai da kayayyakin da sojojin suka kwato, Buba ya ce, an kwato bindiga kirar AK47 guda 62, bindiga mai amon harsasai guda 7, harbi ka noke guda 19, fistol guda 3, wasu bindiga kirar gida guda 10, fistol kirar gida 5, nakiya (IED) guda 399, harsasai masu rai samfurin 7.62mm special ammo guda 225, alburusai samfurin 7.62mm NATO guda 10, alburusai samfurin 9mm ammo guda 13, harsasai 7.62mm x 54mm guda 20, harsasai samfurin cartridges guda 57, 49 magazines, motoci 21, machine hudu, keke-napep daya, wayoyin salula ukulele, da kudi da yawansu ya kai N3,194,450.00.

Kazalika, sojojin da ke aiki a yankin Neja-Delta sun gano gami da tarwatsa gidajen karkashin kasa guda 21, jiragen ruwa 56, tukwanan adana abinci 138, nau’in abun dumama abinci (oven) guda 235, injunan ban ruwa 6, wasu jirgin ruwa guda 2 masu gudun tsiya, haramtatun wuraren tace mai 89 da kudi naira N13,950.

Labarai Masu Nasaba

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

Sannan kuma sojojin sun kamo litar danyen mai 1,205,950 da aka sace, litar gas 452,910, litar man fetur  guda 22,650 da kuma litar kananzir 3,000.

Ya ce, sojoji ba za su daina kokarin da su ke yi ba na dakile aniyar bata gari da ‘yan ta’adda ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaSojoji
ShareTweetSendShare
Previous Post

Lantarki Ya Ɗauke A Faɗin Nijeriya, Yayin Da Tashar Samar Da Wuta Ta Ƙasa Ta Lalace

Next Post

Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Dandalin Tattaunawar Al’adun Beijing Na 2023

Related

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Manyan Labarai

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

55 minutes ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

15 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

18 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

22 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

1 day ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

1 day ago
Next Post
Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Dandalin Tattaunawar Al’adun Beijing Na 2023

Xi Jinping Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Dandalin Tattaunawar Al’adun Beijing Na 2023

LABARAI MASU NASABA

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.