• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wata Sabuwa: Gwamna Ya Kai Karar Shugaban Majalisa Gaban Tinubu Kan Nada Shugabancin Kwamiti Mai Gwabi

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma ya kai karar shugaban majalisar wakilai, Tajudeen Abbas gaban Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu bisa daukaka dan majalisar jiharsa, Ikenga Imo Ugochinyere wajen ba shi kwamiti mai gwabi a cikin gwamnatin jam’iyyar APC. 

Uzodinma ya bayyana rashin jin dadinsa ga Abbas wajen martaba Ugochinyere, wanda ya kasance dan majalisa a karkashin tutur jam’iyyar PDP, na danka masa shugabancin kwamitin man fetur (da aka tace).

  • Remi Tinubu Ta Bada Tallafin Naira Miliyan N500 Ga Iyalai 500 Da Rikici Ya Shafa A Jihar Filato

An bayyana cewa Uzodinma wanda ya kasance shugaban kungiyar gwamnonin APC ya kalubalance nadi bokin hamayyarsa shugaban kwamitin majalisa mai gwabi tun loacin da aka sanar da nadin.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa shugaban majalisar wakilai Abbas ya fusata Uzo-dinma wanda yake ganin cewa wannan nadin zai bai wa Ugochinyere shahara a cikin harkokin siyasa.

Bayan haka kuma, an bayyana cewa gwamnan ya dauki nadin dan majalisar a matsayin shugaban kwamitin mai gwabi za sa dan adawa ya kara karfi a siyasance, wanda hakan cin mutunci ne a matsayinsa na gwamnan jihar kuma shugaban kungiyar gwamnonin APC.

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

Wata majiya da ke kusa da gwamnan ta bayyana cewa, lallai gwamnan ya yi matukar fusata da nadin Ugochinyere wanda hakan zai taba kimarsa a matsayinsa na gwamnan Jihar Imo.

A cewar wata majiyar, Uzodinma ya damu sosai na nadin Ugochinyere shugabancin kwamitin mai gwabi a zauren majalisar wakilai na tarayya, wanda hakan zai kara wa ‘yan adawa karfi a cikin harkokin siyasa.

Duk da dai kotun sauraron kararrakin zabe da ke zamanta a Jihar Nasarawa ta soke zaben Ugochinyere, dan majalisar ya daukaka kara na kalubalantar hukuncin a kotun daukaka kara.

Ugochinyere zai ci gaba da zama dan majalisar wakilai har sai kotun daukaka kara ta zantar da hukunci.

LEADERSHIP ta ruwaito cewa Uzodinma ya yi kokarin shawo kan Abbas kan ya janye nadin.

An samu rahoton da ke cewa shugaban majalisar wakilan ya yi watsi da bukatar gwamnan.

LEADERSHIP ta kuma kara da cewa tuni Uzodinma ya kai karar Abbas gaban Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu kan wannan nadin.

Har ila yau, a nasa martanin, Ugochinyere ya bukaci Uzodinma ya cire Abbas daga ciki siyasar Jihar Imo.

A wata tattaunawa ta wayar tarho, dan majalisar da ke cikin rudani ya bayyana cewa ba sai ya bukaci goyon bayan Abbas ba wajen murkushe Uzodinma a zabe mai zuwa a jihar.

Ya siffanta Uzodimma a matsayin karamin kwaro a siyasa. Ya ce, “Za mu mur-kushe Uzodinma a zaben gwamna a watan Nuwamba kamar yadda muka yi a zaben watan Mayu.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnonimajalisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Kori Kwamishina Kan Kalaman Barazana Ga Alkalai

Next Post

Martanin Obaseki Ga Wike Kan Kiran Dakatar Da Atiku Daga PDP…

Related

Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

2 days ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

2 days ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

2 days ago
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

3 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

3 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

4 weeks ago
Next Post
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili

Martanin Obaseki Ga Wike Kan Kiran Dakatar Da Atiku Daga PDP…

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya Buƙaci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi Yaƙi Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.