• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tasirin Mata A Harkar Hakar Ma’adanai Na Kara Bayyana

byBello Hamza
2 years ago
Mata

A ci gaba da kokarin ganin ba a bar su a baya ba, wasu gungun mata a karkashin inuwar kungiyar ‘Women in Mining in Nigeria (WIMIN)’ sun kafa reshe na 27 a yankin Babban Birnin Tarayya Abuja don shiga a dama da su a harkar hakar ma’adanai a fadin kasar nan.

A bikin kaddamar da shugabanin reshen na Abuja da aka yi a karshen mako, Shugabar kungiyar ta kasa, Dakta Janet Adeyemi, ta ranstar da kwamitin riko wanda Dakta Comfort Asokoro-Ogaji, za ta jagoranta kafin a kai ga zaban shugabanin kungiyar na dindindin.

  • Kungiyar Kasar Sin Ta Lashe Dukkan Lambobin Zinare Na Wasannin Nutso A Gasar Wasannin Kasashen Asiya
  • Barazanar Tsaro: Gwamna Kefas Ya Nemi A Tura Masa Bataliya Zuwa Taraba

A jawabinta a wajen taron, Shugabar kungiyar na kasa, Hon Adeyemi, wadda mai ilimin ma’adanai ne kuma tsohuwar ‘yar majalisar kasa ce, ta bayyana cewa, ta kafa kungiyar ce bayan da ta lura da yadda ake cutar da mata a harkar ma’adanai a Nijeriya, musamman a wuraren hakar ma’adanai na Jos da saurar sassan kasar nan, kuma ana nisantar da su daga shiga cikin harkokin kasuwancin ma’adanai a kasar nan, haka kuma ta fahimci cewa, kwararrun mata masu ilimin hakar ma’adanai na fuskantar wariya ana kuma kange su daga rike mukamai a cibiyoyi da hukumomin gudanar da harkokin ma’adanai na kasa, a kan haka ta kudiri aniyar dawo da martabar mata a harkar hakar ma’adanai a Nijeriya.

Ta kara da cewa, da farko, ta fuskanci turjiya daga maza amma ganin yadda ta dake da aiwatar da kudurinta, a halin yanzu an samu mata da dama da ke aiki a bangaren ma’adanai har an kai ga kafa reshen kungiyar a jihohi 27 cikin jihohi 36 da yankin babbar birnin tarayya, akwai kuma reshen kungiyar a kasashen Afirika da wasu sassan duniya har guda 96.

Ta kuma kara da cewa, in har mata suka hada kai a tsakaninsu, maza ba za su iya zarce su ba, musamman ganin harkar ma’adanai na da bangarori daban-daban da kowa zai iya samun nashi alharin ba tare da takurawa wai ba, tun daga masu haka, sarrfawa da saye da sayarwa da kuma fitarwa kasashen waje.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

A nata jawabin, shugabar kungiyar na yankin Abuja, Dakta Comfort Asokoro-Ogaji, ta ce, za ta tabbatar da amfani da matsayinta wajen bunkasa shigar mata a harkar hakar ma’adanai a yankin Abuja.

A tattaunawar da ta yi da manema labarai, ta ce, Allah ya albarkaci yankin Abuja da ma’adanai masu muhimmanci wadanda suka hada da ‘Gold, Cassiterite, Dolomite, Lead/zinc, Marble da Tantalite’.

Ta yaba wa hukumar yankin babbar birnin Abuja a kan yadda ta kirkiro da sashin na musamman don kula da harkokin ma’adanai wanda hakan zai taimaka a gaggauta samar da aikin yi da arziki ga al’umma.

Dakta Asokoro-Ogaji ta kara da cewa, “A mastayin mu na mata za mu bayar da namu gudummawar wajen aiki a bangaren hakar ma’adanai tare da tabbatar da gwamnati na samun kudaden shiga daga bangaren hakar ma’adanai kamar yadda ya kamata.

“Ya kamata mata a yankjin Abuja su amfana da wadannan albarkatun kasa da Allah ya samar a yankin. Tabbas akwai abubuwan da suke bukatar kudi amma wasu abubuwan suna bukatar jajircewa ne kawai na al’umma, idan kowa ya bayar da nasa gudummawar dole a kai ga ci gaba wanda kuma hakan zai amfanar da al’umma gaba daya.

Bincike ya nuna cewa, mata na bayar da gaggrumin gudumawa a harkar hakar ma’adanai, amma ana amfani dasu ne kawai ba tare da suna cin cikakkiyar gajiyar aikin da suke yi ba. A kan haka aka nemi shugabannin al’umma sarakuna da sauran masu ruwa da tsaki da su tsayu wajen ganin dukkan al’umma na cin gajiyar ma’adanai da Allah ya horewa kasa, ta hanyar amfani da kudaden da ake samu wajen gudanar da ayyuykan ci gaba ga al’umma tare da sa ido don kare muhalli daga cutarwar ayyukan masu hakar ma’adanai.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

October 3, 2025
Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho
Tattalin Arziki

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

October 3, 2025
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG
Tattalin Arziki

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Next Post
Cire Tallafin Mai: Za A Fara Bai Wa Talakawa Dubu 8 Duk Wata

Kungiyar Masu Masana’antu Ta Nemi Gwamnati Ta Daidaita Harajin Da Ake Kakaba Musu

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version