ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 4, Sun Raunata 5 A Kaduna

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Kaduna

Wasu da ake zargin ‘yan fashin daji ne sun mamayi kauyen anguwar Dandali da ke karamar hukumar Zariya a jihar Kaduna tare da kashe mutane hudu da jikkata wasu biyar.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin hakimin kauyen, Mallam Sunusi Yusuf, ya shaida cewar ‘yan bindigar sun isa kauyen ne da karfe misalin 10:30 na daren ranar Juma’a, inda suka fara harbi kan mai uwa da wabi.

  • Burina Kawo Ci Gaban Da Ba A Taba Tunani Ba A Harkar Fim —Ibrahim Ali (2)
  • Yadda Garkuwa Da Dalibai Ke Haifar Da Koma-baya Ga Ci Gaban Ilimi A Arewa

Ya yi bayanin cewa ‘yan bindigar sun samu nasarar harbe mutum tara gami da yin garkuwa da mutane biyar kafin daga bisani jami’an tsaro suka mamaye su wanda hakan ya janyo suka musayar wuta.

ADVERTISEMENT

Ko da yake a cewarsa, duk da zuwan jami’an tsaron hakan bai hana ‘yan bindigar yin garkuwa da wasu ba.

“Daga cikin mutum tara da suka harba, hudu nan take suka mutu, yayin da kuma biyar suka samu raunuka.”

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Wadanda aka kashe sun hada da Dahiru Tsalha Wawo, Bashir Salisu, Umar Yahuza da kuma Umar Bako. Sannan kuma wadanda suka jikkata su ne; Abubakar Yahuza, Bala Shamaki, Aliyu Ahmed, da Abdullahi Mamuda.

An birne wadanda suka rasa rayukansu a makabartar Hayin Dogo, Unguwar Dankali kamar yadda addinin musulunci ya tanadar.

Liman Alhaji Musa Tanko, mai unguwa ne a yankin, ya shaida cewa, al’umma suna cikin firgici da tashin hankali sakamakon yawaitar farmakin da ‘yan bindiga.

“Da farko da ‘yan bindigar na yawan kai hare-hare ne a kauyen Anguwar Dankali, amma yanzu suna mamayar makwafta Wusasa da yankin Kuregu wadanda ‘yan bindiga ke cigaba da kai hare-harensu. Wannan lamarin ya zama abun tashin hankali matuka yayin da ‘yan bindigan ke kara fadada aikace-aikacensu zuwa wasu yankunan,” ya shaida.

Tanko ya yi kiran a dukufa da addu’a domin neman kawo karshen matsalolin tsaro da suke faruwa a yankin.

A lokacin da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yansandan jihar na rikon kwarya, ASP Mansir Hassan, ya yi alkawarin cewa zai tuntubi babban baturen dan sandan yankin, Dan Magaji kuma zai kira daga baya domin bayar da cikakken bayani kan abin da ya faru, amma har zuwa hada wannan rahoto bai kira ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja
Manyan Labarai

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Next Post
Kasar sin

Mutane Miliyan 826 Sun Yi Yawon Shakatawa A Yayin Ranaikun Hutu Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.