• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 4, Sun Raunata 5 A Kaduna

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Kaduna

Wasu da ake zargin ‘yan fashin daji ne sun mamayi kauyen anguwar Dandali da ke karamar hukumar Zariya a jihar Kaduna tare da kashe mutane hudu da jikkata wasu biyar.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin hakimin kauyen, Mallam Sunusi Yusuf, ya shaida cewar ‘yan bindigar sun isa kauyen ne da karfe misalin 10:30 na daren ranar Juma’a, inda suka fara harbi kan mai uwa da wabi.

  • Burina Kawo Ci Gaban Da Ba A Taba Tunani Ba A Harkar Fim —Ibrahim Ali (2)
  • Yadda Garkuwa Da Dalibai Ke Haifar Da Koma-baya Ga Ci Gaban Ilimi A Arewa

Ya yi bayanin cewa ‘yan bindigar sun samu nasarar harbe mutum tara gami da yin garkuwa da mutane biyar kafin daga bisani jami’an tsaro suka mamaye su wanda hakan ya janyo suka musayar wuta.

Ko da yake a cewarsa, duk da zuwan jami’an tsaron hakan bai hana ‘yan bindigar yin garkuwa da wasu ba.

“Daga cikin mutum tara da suka harba, hudu nan take suka mutu, yayin da kuma biyar suka samu raunuka.”

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Wadanda aka kashe sun hada da Dahiru Tsalha Wawo, Bashir Salisu, Umar Yahuza da kuma Umar Bako. Sannan kuma wadanda suka jikkata su ne; Abubakar Yahuza, Bala Shamaki, Aliyu Ahmed, da Abdullahi Mamuda.

An birne wadanda suka rasa rayukansu a makabartar Hayin Dogo, Unguwar Dankali kamar yadda addinin musulunci ya tanadar.

Liman Alhaji Musa Tanko, mai unguwa ne a yankin, ya shaida cewa, al’umma suna cikin firgici da tashin hankali sakamakon yawaitar farmakin da ‘yan bindiga.

“Da farko da ‘yan bindigar na yawan kai hare-hare ne a kauyen Anguwar Dankali, amma yanzu suna mamayar makwafta Wusasa da yankin Kuregu wadanda ‘yan bindiga ke cigaba da kai hare-harensu. Wannan lamarin ya zama abun tashin hankali matuka yayin da ‘yan bindigan ke kara fadada aikace-aikacensu zuwa wasu yankunan,” ya shaida.

Tanko ya yi kiran a dukufa da addu’a domin neman kawo karshen matsalolin tsaro da suke faruwa a yankin.

A lokacin da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yansandan jihar na rikon kwarya, ASP Mansir Hassan, ya yi alkawarin cewa zai tuntubi babban baturen dan sandan yankin, Dan Magaji kuma zai kira daga baya domin bayar da cikakken bayani kan abin da ya faru, amma har zuwa hada wannan rahoto bai kira ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Next Post
Kasar sin

Mutane Miliyan 826 Sun Yi Yawon Shakatawa A Yayin Ranaikun Hutu Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.