ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 4, Sun Raunata 5 A Kaduna

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Kaduna

Wasu da ake zargin ‘yan fashin daji ne sun mamayi kauyen anguwar Dandali da ke karamar hukumar Zariya a jihar Kaduna tare da kashe mutane hudu da jikkata wasu biyar.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin hakimin kauyen, Mallam Sunusi Yusuf, ya shaida cewar ‘yan bindigar sun isa kauyen ne da karfe misalin 10:30 na daren ranar Juma’a, inda suka fara harbi kan mai uwa da wabi.

  • Burina Kawo Ci Gaban Da Ba A Taba Tunani Ba A Harkar Fim —Ibrahim Ali (2)
  • Yadda Garkuwa Da Dalibai Ke Haifar Da Koma-baya Ga Ci Gaban Ilimi A Arewa

Ya yi bayanin cewa ‘yan bindigar sun samu nasarar harbe mutum tara gami da yin garkuwa da mutane biyar kafin daga bisani jami’an tsaro suka mamaye su wanda hakan ya janyo suka musayar wuta.

ADVERTISEMENT

Ko da yake a cewarsa, duk da zuwan jami’an tsaron hakan bai hana ‘yan bindigar yin garkuwa da wasu ba.

“Daga cikin mutum tara da suka harba, hudu nan take suka mutu, yayin da kuma biyar suka samu raunuka.”

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Wadanda aka kashe sun hada da Dahiru Tsalha Wawo, Bashir Salisu, Umar Yahuza da kuma Umar Bako. Sannan kuma wadanda suka jikkata su ne; Abubakar Yahuza, Bala Shamaki, Aliyu Ahmed, da Abdullahi Mamuda.

An birne wadanda suka rasa rayukansu a makabartar Hayin Dogo, Unguwar Dankali kamar yadda addinin musulunci ya tanadar.

Liman Alhaji Musa Tanko, mai unguwa ne a yankin, ya shaida cewa, al’umma suna cikin firgici da tashin hankali sakamakon yawaitar farmakin da ‘yan bindiga.

“Da farko da ‘yan bindigar na yawan kai hare-hare ne a kauyen Anguwar Dankali, amma yanzu suna mamayar makwafta Wusasa da yankin Kuregu wadanda ‘yan bindiga ke cigaba da kai hare-harensu. Wannan lamarin ya zama abun tashin hankali matuka yayin da ‘yan bindigan ke kara fadada aikace-aikacensu zuwa wasu yankunan,” ya shaida.

Tanko ya yi kiran a dukufa da addu’a domin neman kawo karshen matsalolin tsaro da suke faruwa a yankin.

A lokacin da aka tuntubi kakakin rundunar ‘yansandan jihar na rikon kwarya, ASP Mansir Hassan, ya yi alkawarin cewa zai tuntubi babban baturen dan sandan yankin, Dan Magaji kuma zai kira daga baya domin bayar da cikakken bayani kan abin da ya faru, amma har zuwa hada wannan rahoto bai kira ba.

Kaduna
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Kasar sin

Mutane Miliyan 826 Sun Yi Yawon Shakatawa A Yayin Ranaikun Hutu Na Kasar Sin

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.