• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Nuna Bakin Ciki Kan Mutuwar Fararen Hula A Rikicin Falasdinu Da Isra’ila

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Isra'ila
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Mao Ning ta bayyana cewa, kasar Sin ta yi matukar bakin ciki kan yadda fararen hula suka rasa rayukansu, sakamakon rikicin da ya barke tsakanin Falasdinu da Isra’ila, kuma tana adawa da kuma yin tir da ayyukan da ke cutar da fararen hula.

Mao ta bayyana hakan ne yau Litinin din nan a yayin taron manema labarai na yau da kullum don yin karin haske kan rikicin dake faruwa a tsakanin Isra’ila da kungiyoyin Falasdinawa masu dauke da makamai a yankin zirin Gaza, wanda ya janyo hasarar dimbin rayuka a tsakanin bangarorin biyu.

  • Xi Ya Fadawa Schumer Yadda Sin Da Amurka Za Su Daidaita Zai Tabbatar Da Makomar Bil Adama
  • ‘Yan Jarida Sun Yaba Da Ci Gaba Da Al’adun Jihar Xinjiang

Mao ta ce, kasar Sin ta damu matuka game da yadda rikicin Palasdinu da Isra’ila ke ci gaba da rincabewa a baya-bayan nan, kuma ta yi matukar bakin ciki da hasarar rayukan fararen hula da rikicin ya haifar. Tana mai cewa, kasar Sin tana adawa da kuma yin tir da ayyukan da ke cutar da fararen hula.

A cewarta, kasar Sin na adawa da ayyukan da ke kara ta’azzara rikicin da kuma kawo cikas ga zaman lafiyar yankin, tana kuma fatan ganin an tsagaita bude wuta da dawo da zaman lafiya nan da nan. Ta ce, ya kamata kasashen duniya su taka rawar da ta dace da kuma hada kai, don yayyafawa lamarin ruwa.

Sannan, a jiya Lahadi ne kwamitin tsaron MDD ya gudanar da zaman gaggawa na sirri, bayan da dakarun Falasdinawa suka kaddamar da muggan hare-hare kan yankunan Isra’ila dake zirin Gaza.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

Cikin tsokacin da ya yi game da hakan, wakilin dindindin na kasar Sin a MDD Zhang Jun, ya yi kira ga sassan da rikicin ya shafa da su kai zuciya nesa, tare da kaucewa rura wutar rikicin.

Zhang ya kara da cewa, Sin ta yi matukar damuwa bisa dauki ba dadin da ya barke tsakanin sojojin Isra’ila da dakarun Falasdinu a Gaza, wanda hakan ya sabbaba rasuwar fararen hula masu yawa. Ya ce Sin ta damu da yiwuwar kara kazantar fadan.

Daga nan sai jami’in ya jaddada kira ga dukkanin sassan da rikicin ya shafa, da su dakile ta’azzarar fadan, su kuma amincewa matakan tsagaita bude wuta. Kaza lika su rungumi matakan ingiza kafuwar kasashe biyu masu cin gashin kai ba tare da wani bata lokaci ba.

Da yammacin jiya Lahadi, kafofin watsa labaran Isra’ila da dama sun bayyana cewa, sabon fada ya kara rincabewa tsakanin sassan biyu, wanda hakan ya haifar da kisan al’ummar Isra’ila sama da 700.

A daya bangaren kuma, hukumar kiwon lafiya ta Falasdinawa dake zirin Gaza, ta fitar da sanarwa a daren jiyan, wadda a ciki ta bayyana cewa, harin sojojin Isra’ila a zirin na Gaza, ya hallaka a kalla mutane 413 tare da jikkata wasu 2300. (Masu Fassarawa: Ibrahim Yaya, Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FalasdinuHamasIsra'ilawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Fadawa Schumer Yadda Sin Da Amurka Za Su Daidaita Zai Tabbatar Da Makomar Bil Adama

Next Post

Kotu Ta Yanke Wa Jami’in ‘Yansandan Da Ya Harbe Lauya Raheem Hukuncin Kisa A Legas

Related

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

19 hours ago
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

20 hours ago
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana
Daga Birnin Sin

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

21 hours ago
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa
Daga Birnin Sin

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

22 hours ago
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
Daga Birnin Sin

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

23 hours ago
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su
Daga Birnin Sin

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

2 days ago
Next Post
Kisa

Kotu Ta Yanke Wa Jami'in 'Yansandan Da Ya Harbe Lauya Raheem Hukuncin Kisa A Legas

LABARAI MASU NASABA

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

Zaben 2027 Yaƙi Ne Tsakanin Talakawa Da Masu Mulki – Sanata Kaita 

June 29, 2025
Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

Gyaran Tsarin Mulki: Majalisa Ta Shirya Sauraron Jin Ra’ayoyin Jama’a A Wasu Sassan Nijeriya

June 29, 2025
Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

Yara 150,000 Ake Haifa Da Cutar Sikila A Nijeriya Duk Shekara – Rahoto

June 29, 2025
Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

Mutuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Nijeriya – Gov Ododo

June 29, 2025
Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

Jirgin Alhazai Na Farko Ya Iso Jihar Jigawa

June 29, 2025
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

June 29, 2025
Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.