ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalibai Mata 16,260 Za Su Fara Cin Gajiyar Tallafin Karatu Na N5,000, Da N10, 000 A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Dalibai Mata

A wani bangare na kokari tallafa wa yara mata kan harkar ilimi, ta cikin shirin tallafa wa karatun ‘ya’ya mata a Jihar Bauchi (AGILE) za a fara bai wa ‘yan mata a kananan makarantu da sakandire N5,000 da N10,000 don tallafa musu a harkar karatu da ba su damar zuwa makaranta a kan lokaci. 

Kimanin ‘yan mata 16,260 a fadin Bauchi ne za su ci gajiyar shirin, domin cimma nasarar shirin, kowace Daliba ana so ta samu kashi 80 cikin 100 na zuwa makaranta a kowane zango.

  • Kungiya Ta Nemi ‘Yan Adawa Su Rungumi Kaddara Kan Hukuncin Kotun Zaben Gwamnan Bauchi
  • Za Mu Tabbatar An Hukunta Masu Zaluntar Kananan Yara Da Mata – Kwamishina Rabi Salisu

Ko’odinetan shirin AGILE kuma kwamishiniyar ilimi ta jihar, Dakta Jamila Muhammad Dahiru ce ta bayyana hakan ga manema labarai a karshen makon da ya gabata yayin wata tattaunawa da manema labarai a ofishinta.

ADVERTISEMENT

Ta ce za a rika biyan kudin ne a kowane zango domin karfafa wa dalibai guiwa su rika zuwa makaranta a ko da yaushe.

Ta kara da cewa, ana shirye-shiryen koyar da ilimin fasahar zamani don karfafawa ‘yan mata masu fasahar ilimin na’ura (ICT) damar sanya su zama masu dogaro da kansu da kuma ci gaba da neman ilimi a manyan makarantu.

LABARAI MASU NASABA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

Jamila ta ce, shirin na AGILE yana da burin yin abubuwa daban-daban domin tallafawa fannin ilimi ta hanyar inganta tsarin ilmantarwa a cikin yanayi mai kyau.

Ta kuma jaddada cewa, wannan shirin an yi shi ne don karfafawa ‘ya’ya mata da suka daina zuwa makaranta saboda matsalar tattalin arziki samun damar komawa makaranta su kammala matakin neman ilmin su.

AGILE – shiri ne da ya fito karkashin Bankin Duniya na Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya wanda aka tsara don inganta Ilimin Sakandare ga ‘yan mata ‘yan tsakanin shekaru 10 zuwa 20.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
Manyan Labarai

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS
Labarai

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS
Labarai

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
Next Post
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayanai Game Da Hadin Gwiwar Ziri Daya Da Hanya Daya

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayanai Game Da Hadin Gwiwar Ziri Daya Da Hanya Daya

LABARAI MASU NASABA

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.