• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Yamma Suna Tsotse Jinin ‘Yan Afirka Yayin Da Kasar Sin Ke Kawo Bege

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kasashen Yamma Suna Tsotse Jinin ‘Yan Afirka Yayin Da Kasar Sin Ke Kawo Bege
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana wawushe albarkatun Kasa da ma’adinai, ana kwace ’yancin mallakar kasa, ana zaluntar mutane. Wannan ita ce mummunar fahimta da da’awar da kafofin yada labarai na kasashen yamma suke yadawa game da shirin shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya ko BRI a takaice. A wajensu, BRI na nufin “farauta” da “tsangwama.”

An ce wanzami ba ya son jarfa, a hakikanin gaskiya wannan kage da kasashen yamma suka yiwa shirin BRI da nufin muzgunawa kasar Sin na bayyana ainihin illoli wadanda suka hada da mamaya, katsalandan, tsangwama da babakeren da Amurka da kawayenta na yamma suka yiwa kasashen Afirka ne.

  • Ganawa Da Xi Jinping: Ina Godiya Gare Shi Bisa Cimma Burina
  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Zai Halarci Bikin Bude Taron BRF

Bari mu kawo wasu misalai sa’annan mu kwatanta bangarorin biyu, za mu fahimci wace kasa ce ke “farautar Afirka da tsangwama mata” tsakanin kasar Sin da Amurka da kawayenta na yamma. Kasar Amurka ta kafa sansanonin sojoji 29 a nahiyar Afirka yayin da kasar Sin take da daya a Djibouti. Amma duk da haka Amurka na ikirarin cewa Sin ce ke yin katsalandan a nahiyar.

Gaskiya ne cewa kasar Sin na gina layin dogo a duk fadin Afirka wanda Joe Biden shugaban ƙasar Amurka ya yi mafarkin cewa Amurka za ta gina, a maimakon haka, shugabannin na Amurka sai tofin Allah wadai da ayyukan Sinawa a Afirka suke ke yi, alhalin a duk ziyararsu a Afirka alal akalli sai sun sauka a wani filin jirgin saman Afirka da Sin ta gina, su kuma shiga cikin gari a kan wata babbar hanyar da kasar Sin ta shimfida. Wannan shi ne ake ce ma munafurcin dodo ya kan ci mai shi.

To wai shin mene ne shisshigi kuma mene ne ci gaba? Kasar Sin ta shiga Afirka lungu da sako tana taimakawa wajen gina ababen more rayuwa da Turawan mulkin mallaka ba su taba ginawa ba, da kuma taimakawa wajen gina makomar tattalin arziki mai cin gashin kanta bayan mulkin mallaka, wanda kasashen yammacin duniya suka yi duk mai yiwuwa don hanawa.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Kasar Sin ba ta bautar da kowa a Afirka ba kuma kasar Sin ba ta mamaye ko’ina a Afirka ba. Amma babu wata kasa a nahiyar Afirka da kasashen yamma ba su debi magabatanmu a matsayin bayi zuwa kasashensu suka bautar da su ba. Kana, babu wani inchin murabba’i na kasa da mulkin mallakar yamma bai mamaye ba.

Wane ne ya taba kashe shugabannin kasashen Afirka? Kasar Sin ba ta yi juyin mulki ba a Afirka. Hasali ma, Sin ba ta tsoma baki a harkar shugabancin kasashen waje, wannan ka’ida ce ta Sin. Ba sai na tunashe mu ta’adin da kasar Amurka ta aikata a kasar Libya zuwa Timbuktu, ko kasar Laberiya zuwa Congo ba.

Kasar Sin ba ta taba goyon bayan wariyar launin fata a Rhodesia da Afirka ta Kudu ba. Sabanin haka, kasar Sin ta goyi bayan gwagwarmayar ‘yanci a dukkan bangarorin biyu. Yamma ce ta rura wutar fitinar wariyar launin fata da ta samu tushe a tarihin kasashen biyu.

Ba kasar Sin ce ta karya farashin Uranium na Nijar zuwa wajen Yuro 0.1 kan ko wane kilogiram ba, a lokacin da farashin a kasuwa ya kai wajen Yuro 25 kan kowane kilogiram na Uranium daga Nijar. Har ila yau, wannan shi ma makircin yamma ne.

Shirin shawarar “ziri daya da hanya daya” na kasar Sin yana shimfida hanyoyin mota, layin dogo da habaka sufurin jiragen sama, da gina makarantu, asibitoci, jami’o’i da makarantun kananan yara.

Su kuma kasashen yamma na totse jinin ’yan Afirka kamar yadda suka yi shekaru aru-aru da suka gabata, yayin da kasar Sin ke kawo bege. Wannan shi ne bambanci tsakanin Sin da kasashen Yamma. (Muhammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaSinXi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shawarar BRI Ta Kawo Manyan Sauye-sauye A Duniya Cikin Shekaru 10 Da Suka Gabata

Next Post

NIS Ta Shirya Taro A Kan Alfanun Tattalin Arzikin Teku Ga Manyan ‘Yan Kasuwa A Ribas

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

12 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

13 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

14 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

15 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

16 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

1 day ago
Next Post
Nis

NIS Ta Shirya Taro A Kan Alfanun Tattalin Arzikin Teku Ga Manyan 'Yan Kasuwa A Ribas

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.