• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sin Ta Kafa Kyakkyawan Misali A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ga duk mai bibiyar al’amuran yau da kullum dake gudana a matakin kasa da kasa, ya kwana da sanin cewa, kasar Sin ta sake samun gurbi a hukumar kare hakkin bil adama ta MDD, sakamakon zabenta da aka sake yi, yayin taron koli na MDD da ya gudana a ’yan kwanakin baya, kuma bisa hakan, za ta kasance cikin mambobin hukumar tun daga shekarar 2024 dake tafe har zuwa 2026.

Wannan ne karo na shida, da Sin din ke samun damar ba da gudummawa a wannan hukuma ta MDD, tun bayan kafuwarta a shekarar 2006. To ko mene ne ya sanya har yanzu ake damawa da kasar Sin a wannan hukuma mai muhimmanci?

  • Sin Ta Kadu Ta Yi Tir Da Kisan Jama’a Masu Tarin Yawa Sakamakon Hari Kan Asibiti A Gaza 
  • Yadda Kasar Sin Ke Ba Da Gudummawar Zamanintar Da Kasashen Duniya Cikin Shekaru 10 Masu Zuwa

Hakika dalilan suna da yawa, amma kadan daga cikinsu su ne gamsuwar da sassan kasa da kasa suka yi, da irin nasarorin da Sin din ta cimma a bangarorin kare hakkokin bil adama a cikin gida, da ma yadda take taka rawar gani wajen shiga hadin gwiwar kare hakkin bil adama a matakin kasa da kasa.

Sanin kowa ne cewa, a matsayinta na daya daga cikin kasashe mambobin farko na MDD, kuma mai kujerar dindindin a majalissar, har kullum kasar Sin na shiga dukkanin ayyukan da suka shafi kare hakkin bil adama, tana sauke nauyin tallafawa ayyukan da suka shafi hakan, kana tana goya baya ga tsarin jagoranci na kare hakkokin bil adama yadda ya kamata.

Har ila yau, duniya ta gamsu da yadda Sin din ke ingiza duk wasu matakai na samun ci gaban manufofin kare hakkin bil adama cikin lumana kuma a dukkanin matakai.

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Kaza lika, Sin na martaba ka’idojin MDD, da sauran kudurorin da sassan kasa da kasa suka amince da su game da kare hakkin bil adama, wanda hakan ya sanya ta zama abun koyi ga sauran sassan duniya a wannan fage.

A ganin kasar Sin, kare martabar al’umma shi ne babban jigo na tabbatar da hakkokin bil adama, wato dai farin cikin al’umma shi ne kan gaba, idan ana batun kare hakkin bil Adama.

Ko shakka babu, al’ummar kasar Sin na kara cin gajiya daga nasarorin kasarsu, kuma Sin na sanya bukatun jama’a gaban komai, tana goyon bayan duk wasu tsare-tsare na samar da ci gaban al’umma daga dukkanin fannoni, ta yadda duniya ke yabawa, da irin gudummawarta a bangaren kare hakkokin bil Adama. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FalasdinuIsra'ilawa
ShareTweetSendShare
Previous Post

NYSC Ta Yi Jimami Kan Kisan ‘Yar Hidimar Kasa A Kaduna

Next Post

Na Sha Alwashin Magance Talauci Da Kashi 80 Cikin 100 A Jihata – Gwamnan Kaduna

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

2 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

4 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

4 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

8 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

10 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

10 hours ago
Next Post
Kaduna

Na Sha Alwashin Magance Talauci Da Kashi 80 Cikin 100 A Jihata - Gwamnan Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.