• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kashe Mutane Biyar, Fursunoni 879 Sun Tsere A Harin Gidan Yarin Kuje – Gwamnati

by Sadiq
3 years ago
Kuje

Hukumar da ke kula da gidajen yari ta Nijeriya (NCoS), ta ce wani jami’in hukumar tsaron farin kaya ta Nijeriya (NSCDC), ya mutu a lokacin da ‘yan bindiga suka kai hari gidan yarin Kuje da ke Abuja a daren ranar Talata.

Kakakin Hukumar NCoS, Umar Abubakar ne, ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a Abuja a ranar Laraba.

  • Yanzu-yanzu: Abba Kyari Bai Bace Daga Gidan Yari Kuje Ba, Cewar Hukuma
  • Zargin Badakalar Kudade: ICPC Ta Cafke Dan Kwangilar Kotun Koli Na Bogi

A cewarsa, an kuma kashe fursunoni hudu a harin da ya dauki tsawon sa’o’i.

Ya ce maharan da suka yi amfani da ababen sun shiga ta babbar kofar shiga da kuma katangar ginin, sun kuma jikkata wasu jami’an hukumar uku.

“Jimillar fursunoni 879 ne suka tsere daga gidan yarin a lokacin da aka kai harin.

LABARAI MASU NASABA

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

“Ya zuwa lokacin hada wannan rahoton, an sake cafke 443, fursunoni 551 na tsare a halin yanzu, fursunoni 443 sun tsare, fursunoni 4 sun mutu, fursunoni 16 kuma sun samu raunuka, inda ake kula da su a halin yanzu.

“Duk da haka, ana ci gaba da kokarin cafke duk fursunonin da suka gudu,” in ji Abubakar.

Ya ce ya zuwa lokacin da aka kai harin a gidan yarin na Kuje, jami’an soji 38 ne a kasa baya ga jami’an ‘yan sandan Nijeriya, Civil Defence da na DSS.

Ya kuma tabbatar da cewa DCP Abba Kyari da sauran manyan jami’an tsaro da ake tsare da su a gidan yarin ba su tsere ba, inda ya ce “A halin yanzu suna hannu, ba su tsere ba”.

Yayin da yake bayyana cewa an kashe wasu daga cikin maharan yayin da wasu suka tsere da raunukan harbin bindiga, Abubakar ya yi kira ga “asibitoci da sauran cibiyoyin kiwon lafiya da likitoci da su kai rahoton duk wanda ya zo musu domin jinyar raunin harbin bindiga ga jami’an tsaro mafi kusa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kuje
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Next Post
Sakataren Jin Dadin Alhazai Na Neja Ya Hana Shugaban Hukumar Na Kasa Hawa Jirgi Tafiya Saudiyya

Sakataren Jin Dadin Alhazai Na Neja Ya Hana Shugaban Hukumar Na Kasa Hawa Jirgi Tafiya Saudiyya

LABARAI MASU NASABA

Kuje

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.