• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kimiyya Ba Dabarar Takara Ba Ce

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kimiyya Ba Dabarar Takara Ba Ce
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shahararriyar mujallar kimiyya da fasaha ta kasar Birtaniya “Nature” ta watsa wani bayani a shafinta na yanar gizo a kwanan nan cewa, kasar Sin a karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, tana kokarin zurfafa hadin gwiwarta da sauran kasashe a fannin nazarin kimiyya da fasaha, da zummar daga matsayin wannan bangare a duk duniya. Kana a cikin bayanin, an yi kira ga kasashen Turai da kasar Amurka da su daina nuna son zuciya, su yi kokarin hada gwiwa da Sin a fannin kimiyya da fasaha, ta yadda za a taimaki dan Adam wajen tinkarar kalubalolin da suke fuskanta a fannonin siyasa, da tattalin arizki, da kuma muhalli.

Na yarda da ra’ayin marubucin wannan bayani, saboda ya nuna sanin ya kamata. Ko da yake yanzu a kasashen yamma, mutane su kan nuna tsattsauran ra’ayi a fannin siyasa, amma duk da haka marubucin ya bayyana gaskiya game da gudunmowar da kasar Sin ta samar wa bangaren kimiyya da fasaha na duniya. Kana hakan ya shaida cewa, nasarorin da kasar Sin ta cimma a wannan fanni, ba abun da za a iya boyewa ba ne.

  • Shugaban CMG Ya Gana Da Shugaban Dandalin Tattauna Tattalin Arzikin Duniya
  • Sin Ta Gabatar Da ’Yan Sama Jannatin Da Za a Harba A Kumbon Shenzhou-17

A ra’ayin kasar Sin, tushen hulda da sauran kasashe shi ne, bude kofa, da ganin dukkan bangarori daban daban sun amfana. A bisa wannan ra’ayi ne, kasar Sin take kokarin hadin gwiwa da mabambantan kasashe don raya kimiyya da fasaha.

Ya zuwa karshen watan Yunin shekarar 2023, kasar Sin ta kulla yarjejeniyoyin hadin gwiwa a fannin kimiyya da fasaha tare da kasashe fiye da 80, karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya. Kana kawancen kungiyoyin kimiyya na Ziri Daya da Hanya Daya, wanda ke da hedkwata a cibiyar nazarin kimiyya ta Sin, ya samar da tallafi ga mambobin kawancen 67 na kasashe 48 don su gudanar da ayyukan bincike.

Cikin shekaru 10 bayan gabatar da shawarar Ziri Daya da Hanya Daya a shekarar 2013, kasar Sin ta gayyaci matasa masu nazarin kimiyya da fasaha fiye da dubu 10, daga kasashe daban daban zuwa kasar, don gudanar da aikin nazari da musayar ra’ayi, kana aka horar da kwararru masu fasahohi da jami’ai fiye da dubu 16. Ban da haka, Sin ta kafa dandalin mika fasahohi 9, a yankunan kudu maso gabashin Asiya, da kudancin nahiyar Asiya, da kasashen Larabawa, da nahiyar Afirka, da yankin Latin Amurka. Ta kuma taimakawa kasashe fiye da 50 dake nahiyar Afirka kafa cibiyar nuna fasahohin noma. Kana kasar ta yi hadin gwiwa da mabambantan kasashe wajen kafa dakunan gwajin fasahohi na Ziri Daya da Hanya Daya fiye da 50, wadanda suka shafi harkokin aikin noma, da sabbin makamashi, da kiwon lafiya, da dai sauransu. Sa’an nan, a wajen taron koli na hadin gwiwar kasa da kasa karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya karo na 3, da aka kawo karshensa a kwanan baya, kasar Sin ta tabbatar da cewa, za ta kara adadin dakunan gwajin zuwa 100, nan da shekaru 5 masu zuwa.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Sai dai idan mun duba matakan da wasu kasashen yamma ke dauka, za mu ga yadda suke hana ruwa gudu ga aikin hadin kan kasa da kasa ta fuskar kimiyya da fasaha. Inda su kan dauki matakin hana yaduwar fasahohi, da magance fitar da wasu kayayyakin fasahohi zuwa ketare, har ma ya kai ga neman gurgunta kamfanonin kimiyya da fasaha na sauran kasashe, da hana cudanyar kwararru masu nazarin kimiyya da fasaha. A ganin wadannan kasashen, kimiyya da fasaha suna da matukar muhimmanci wajen takara da sauran kasashe, kana suna dogaro kan fasahohi masu ci gaba wajen kiyaye tsare-tsaren duniya na yanzu, da kare gibin dake tsakaninsu da mafi yawan kasashe ta fuskar tattalin arziki. Don haka, sam ba su son raba kimiyya da fasaha da sauran kasashe.

Wannan bambancin ra’ayi da ake samu tsakanin kasashen yamma da kasar Sin wani babban dalili ne da ya sa kasashen yamma kallon kasar Sin tamkar abokiyar gaba. Kasashen yamma na kokarin kare matsayinsu na jagorantar tattalin arzikin duniya, da mai tsara ka’idojin kasa da kasa, ta yadda za su iya more sakamakon ci gaban duniya su kadai. Amma kasar Sin ta ce, “Hakan bai yi daidai ba, ya kamata mu ba mabambantan kasashe damar cin moriya da samun ci gaba tare.” Wannan ra’ayi na Sin, a ganin kasashen yamma, tamkar raunana moriyarsu ta tushe ne.

Hakika kimiyya da fasaha sakamako ne na ci gaban al’ummar dan Adam, don haka ya kamata a yi amfani da su wajen amfanawa daukacin dan Adam, maimakon yin mummunar takara da su. Idan su ‘yan siyasa da manyan ‘yan kasuwa na kasashen yamma suka nuna sanin ya kamata, kamar yadda marubucin bayanin mujallar Nature ya yi, da tsara matakai bisa la’akari da moriyar daukacin dan Adam maimakon ta kansu kadai, tare da shiga cikin yunkurin kasar Sin na tabbatar da ci gaban duniya baki daya, to, tabbas za a samu ci gaban harkokin duniyarmu da daidaituwar al’amura cikin sauri. Sai dai ko za su iya yin haka? (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaHausaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 6, Sun Kwato AK-47 Da Babura A Yobe

Next Post

Kasar Sin Ta Dogara Ne Kan Gaskiya Da Adalci, Za Ta Kuma Ba Da Karin Taimakon Jin Kai Zuwa Gaza

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

16 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

17 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

19 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

20 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

1 day ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

1 day ago
Next Post
Kasar Sin Ta Dogara Ne Kan Gaskiya Da Adalci, Za Ta Kuma Ba Da Karin Taimakon Jin Kai Zuwa Gaza

Kasar Sin Ta Dogara Ne Kan Gaskiya Da Adalci, Za Ta Kuma Ba Da Karin Taimakon Jin Kai Zuwa Gaza

LABARAI MASU NASABA

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.