ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kimiyya Ba Dabarar Takara Ba Ce

by CGTN Hausa
3 years ago
Kimiyya

Shahararriyar mujallar kimiyya da fasaha ta kasar Birtaniya “Nature” ta watsa wani bayani a shafinta na yanar gizo a kwanan nan cewa, kasar Sin a karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya, tana kokarin zurfafa hadin gwiwarta da sauran kasashe a fannin nazarin kimiyya da fasaha, da zummar daga matsayin wannan bangare a duk duniya. Kana a cikin bayanin, an yi kira ga kasashen Turai da kasar Amurka da su daina nuna son zuciya, su yi kokarin hada gwiwa da Sin a fannin kimiyya da fasaha, ta yadda za a taimaki dan Adam wajen tinkarar kalubalolin da suke fuskanta a fannonin siyasa, da tattalin arizki, da kuma muhalli.

Na yarda da ra’ayin marubucin wannan bayani, saboda ya nuna sanin ya kamata. Ko da yake yanzu a kasashen yamma, mutane su kan nuna tsattsauran ra’ayi a fannin siyasa, amma duk da haka marubucin ya bayyana gaskiya game da gudunmowar da kasar Sin ta samar wa bangaren kimiyya da fasaha na duniya. Kana hakan ya shaida cewa, nasarorin da kasar Sin ta cimma a wannan fanni, ba abun da za a iya boyewa ba ne.

  • Shugaban CMG Ya Gana Da Shugaban Dandalin Tattauna Tattalin Arzikin Duniya
  • Sin Ta Gabatar Da ’Yan Sama Jannatin Da Za a Harba A Kumbon Shenzhou-17

A ra’ayin kasar Sin, tushen hulda da sauran kasashe shi ne, bude kofa, da ganin dukkan bangarori daban daban sun amfana. A bisa wannan ra’ayi ne, kasar Sin take kokarin hadin gwiwa da mabambantan kasashe don raya kimiyya da fasaha.

ADVERTISEMENT

Ya zuwa karshen watan Yunin shekarar 2023, kasar Sin ta kulla yarjejeniyoyin hadin gwiwa a fannin kimiyya da fasaha tare da kasashe fiye da 80, karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya. Kana kawancen kungiyoyin kimiyya na Ziri Daya da Hanya Daya, wanda ke da hedkwata a cibiyar nazarin kimiyya ta Sin, ya samar da tallafi ga mambobin kawancen 67 na kasashe 48 don su gudanar da ayyukan bincike.

Cikin shekaru 10 bayan gabatar da shawarar Ziri Daya da Hanya Daya a shekarar 2013, kasar Sin ta gayyaci matasa masu nazarin kimiyya da fasaha fiye da dubu 10, daga kasashe daban daban zuwa kasar, don gudanar da aikin nazari da musayar ra’ayi, kana aka horar da kwararru masu fasahohi da jami’ai fiye da dubu 16. Ban da haka, Sin ta kafa dandalin mika fasahohi 9, a yankunan kudu maso gabashin Asiya, da kudancin nahiyar Asiya, da kasashen Larabawa, da nahiyar Afirka, da yankin Latin Amurka. Ta kuma taimakawa kasashe fiye da 50 dake nahiyar Afirka kafa cibiyar nuna fasahohin noma. Kana kasar ta yi hadin gwiwa da mabambantan kasashe wajen kafa dakunan gwajin fasahohi na Ziri Daya da Hanya Daya fiye da 50, wadanda suka shafi harkokin aikin noma, da sabbin makamashi, da kiwon lafiya, da dai sauransu. Sa’an nan, a wajen taron koli na hadin gwiwar kasa da kasa karkashin shawarar Ziri Daya da Hanya Daya karo na 3, da aka kawo karshensa a kwanan baya, kasar Sin ta tabbatar da cewa, za ta kara adadin dakunan gwajin zuwa 100, nan da shekaru 5 masu zuwa.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sai dai idan mun duba matakan da wasu kasashen yamma ke dauka, za mu ga yadda suke hana ruwa gudu ga aikin hadin kan kasa da kasa ta fuskar kimiyya da fasaha. Inda su kan dauki matakin hana yaduwar fasahohi, da magance fitar da wasu kayayyakin fasahohi zuwa ketare, har ma ya kai ga neman gurgunta kamfanonin kimiyya da fasaha na sauran kasashe, da hana cudanyar kwararru masu nazarin kimiyya da fasaha. A ganin wadannan kasashen, kimiyya da fasaha suna da matukar muhimmanci wajen takara da sauran kasashe, kana suna dogaro kan fasahohi masu ci gaba wajen kiyaye tsare-tsaren duniya na yanzu, da kare gibin dake tsakaninsu da mafi yawan kasashe ta fuskar tattalin arziki. Don haka, sam ba su son raba kimiyya da fasaha da sauran kasashe.

Wannan bambancin ra’ayi da ake samu tsakanin kasashen yamma da kasar Sin wani babban dalili ne da ya sa kasashen yamma kallon kasar Sin tamkar abokiyar gaba. Kasashen yamma na kokarin kare matsayinsu na jagorantar tattalin arzikin duniya, da mai tsara ka’idojin kasa da kasa, ta yadda za su iya more sakamakon ci gaban duniya su kadai. Amma kasar Sin ta ce, “Hakan bai yi daidai ba, ya kamata mu ba mabambantan kasashe damar cin moriya da samun ci gaba tare.” Wannan ra’ayi na Sin, a ganin kasashen yamma, tamkar raunana moriyarsu ta tushe ne.

Hakika kimiyya da fasaha sakamako ne na ci gaban al’ummar dan Adam, don haka ya kamata a yi amfani da su wajen amfanawa daukacin dan Adam, maimakon yin mummunar takara da su. Idan su ‘yan siyasa da manyan ‘yan kasuwa na kasashen yamma suka nuna sanin ya kamata, kamar yadda marubucin bayanin mujallar Nature ya yi, da tsara matakai bisa la’akari da moriyar daukacin dan Adam maimakon ta kansu kadai, tare da shiga cikin yunkurin kasar Sin na tabbatar da ci gaban duniya baki daya, to, tabbas za a samu ci gaban harkokin duniyarmu da daidaituwar al’amura cikin sauri. Sai dai ko za su iya yin haka? (Bello Wang)

Kimiyya
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Kasar Sin Ta Dogara Ne Kan Gaskiya Da Adalci, Za Ta Kuma Ba Da Karin Taimakon Jin Kai Zuwa Gaza

Kasar Sin Ta Dogara Ne Kan Gaskiya Da Adalci, Za Ta Kuma Ba Da Karin Taimakon Jin Kai Zuwa Gaza

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.