• English
  • Business News
Friday, August 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jiragen Yaki Sun Kashe ‘Yan Bindiga 42 A Katsina

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Jiragen Yaki Sun Kashe ‘Yan Bindiga 42 A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rundunar Sojin Sama ta Operation Hadarin Daji ta kashe ‘yan ta’adda 42 a kusa da kauyukan Zakka da Umadan a karamar hukumar Safana ta Jihar Katsina.

A cewar majiyar sojin, wani jirgin saman yakin Nijeriya a yayin da ya ke shawagi a sama, ya samu bayanan sirrin ganin ‘yan ta’adda a tsakanin kauyukan Zakka da Umadan.

  • Harin Kuje: Buhari Ya Nuna Rashin Jin Dadinsa Kan Tsaron Kasar Nan
  • Da Dumi-Dumi: Mune Muka Kai Hari Gidan Yarin Kuje – ISWAP

Wannan dai na zuwa ne a yayin da ‘yan ta’addan suka kai hari ofishin ‘yan sanda da ke kauyen Zakka a baya-bayan da ke Dutsenma tare da harbe wani jami’in ‘yan sanda har lahira.

A ranar Talata ne ‘yan ta’addan suka kai hari kan ayarin motocin shugaban kasa a jihar.

Wani babban jami’in rundunar sojin sama, ya ce an gano ‘yan ta’adda a wani kauye mai tazarar kilomita 7.1 daga yammacin garin Safana da kuma yammacin kauyen Yartuda.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

Ya kara da cewa an kuma ga wasu mutanen garin na guduwa daga kauyen saboda ‘yan ta’addan sun yi awon gaba da wasu daga cikin mutanen garin.

“An yi sa’a, kamar yadda aka yi tsammani, daga baya an ga wadanda aka yi garkuwa da su suna tserewa bayan nasarar da jirgin NAF ya samu na kashe maharan.

“Abin da ya biyo bayan harin ta sama shi ne an ga wasu daga cikin mutanen kauyen da suka watse a lokacin da ‘yan ta’addan suka fara mamaye kauyen suna dawowa.

“Mutanen kauyen sun kuma tabbatar da cewa an kawar da ‘yan ta’adda sama da 24 a hare-hare da aka kai ta sama,” in ji majiyar.

“Saboda haka, an aike da wani jirgin yakin zuwa yankin gaba daya, inda ya ci gaba da shawagi a yankin har zuwa safiyar ranar 6 ga Yuli, 2022.

“Bayan ganin yadda ‘yan ta’adda kusan 18 suka taru a wurin, jirgin ya kai hari. An yi nasarar kashe da dama daga cikinsu.

“Sakamakon da aka samu ya nuna cewa harin ya yi daidai kuma an yi nasara.

“Har yanzu ana ci gaba da kokarin gano tare da lalata sauran maboyar ‘yan ta’addan da ke cikin Katsina da kuma Arewa maso Yamma baki daya,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan ta'addaHariJirgin Saman YakiKatsinaNAF
ShareTweetSendShare
Previous Post

Harin Kuje: Buhari Ya Nuna Rashin Jin Dadinsa Kan Tsaron Kasar Nan

Next Post

Buhari Ya Fusata Game Da Harin Gidan Yarin Kuje, Yana Bukatar Amsa

Related

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

2 minutes ago
An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano
Labarai

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

2 hours ago
Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

3 hours ago
Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

4 hours ago
Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara
Manyan Labarai

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

5 hours ago
Kamfani
Manyan Labarai

‘Yan Majalisa Na Amsar Cin Hanci Har Naira Miliyan 3 Kafin Su Gabatar Da Wani Ƙudiri – Kamfani.

19 hours ago
Next Post
Buhari Ya Fusata Game Da Harin Gidan Yarin Kuje, Yana Bukatar Amsa

Buhari Ya Fusata Game Da Harin Gidan Yarin Kuje, Yana Bukatar Amsa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

Sojoji Sun Ceto Shugaban Fulani, Mutane 5 Daga Hannun Ƴan Bindiga A Kogi

August 15, 2025
Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah

Cire Tallafin Mai Ya Taimaka Mana Wajen Aiwatar da Ayyuka, In Ji Gwamna Mbah

August 15, 2025
NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta

August 15, 2025
An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

An Taƙaita Zirga-Zirga A Ƙananan Hukumomi 4 Kafin Zaben Cike Gurbi A Kano

August 15, 2025
Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

Manufofin Hulda Da Kasashen Wajen Da Nijeriya Ke Bukata

August 15, 2025
Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

Shugaba Tinubu Ya Naɗa Sabon Darakta-Janar Na NTA Da Wasu Daraktoci

August 15, 2025
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

August 15, 2025
Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

Bayan Gargadi Daga Gwamnatin Tarayya: Jihohin Arewa 15 Sun Fara Daukar Matakan Dakile Ambaliyar Ruwa

August 15, 2025
Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

Matsalar Shugabanci A Jihohi Ke Haifar Da Rashin Abinci Mai Gina Jiki Ga Yara

August 15, 2025
Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

Ba Sulhu Ko Sassauci Ga Ƴan Bindiga A Zamfara – Gwamna Lawal Dare

August 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.