ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jiragen Yaki Sun Kashe ‘Yan Bindiga 42 A Katsina

by Sadiq
3 years ago
Jiragen Yaki

Rundunar Sojin Sama ta Operation Hadarin Daji ta kashe ‘yan ta’adda 42 a kusa da kauyukan Zakka da Umadan a karamar hukumar Safana ta Jihar Katsina.

A cewar majiyar sojin, wani jirgin saman yakin Nijeriya a yayin da ya ke shawagi a sama, ya samu bayanan sirrin ganin ‘yan ta’adda a tsakanin kauyukan Zakka da Umadan.

  • Harin Kuje: Buhari Ya Nuna Rashin Jin Dadinsa Kan Tsaron Kasar Nan
  • Da Dumi-Dumi: Mune Muka Kai Hari Gidan Yarin Kuje – ISWAP

Wannan dai na zuwa ne a yayin da ‘yan ta’addan suka kai hari ofishin ‘yan sanda da ke kauyen Zakka a baya-bayan da ke Dutsenma tare da harbe wani jami’in ‘yan sanda har lahira.

ADVERTISEMENT

A ranar Talata ne ‘yan ta’addan suka kai hari kan ayarin motocin shugaban kasa a jihar.

Wani babban jami’in rundunar sojin sama, ya ce an gano ‘yan ta’adda a wani kauye mai tazarar kilomita 7.1 daga yammacin garin Safana da kuma yammacin kauyen Yartuda.

LABARAI MASU NASABA

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

Ya kara da cewa an kuma ga wasu mutanen garin na guduwa daga kauyen saboda ‘yan ta’addan sun yi awon gaba da wasu daga cikin mutanen garin.

“An yi sa’a, kamar yadda aka yi tsammani, daga baya an ga wadanda aka yi garkuwa da su suna tserewa bayan nasarar da jirgin NAF ya samu na kashe maharan.

“Abin da ya biyo bayan harin ta sama shi ne an ga wasu daga cikin mutanen kauyen da suka watse a lokacin da ‘yan ta’addan suka fara mamaye kauyen suna dawowa.

“Mutanen kauyen sun kuma tabbatar da cewa an kawar da ‘yan ta’adda sama da 24 a hare-hare da aka kai ta sama,” in ji majiyar.

“Saboda haka, an aike da wani jirgin yakin zuwa yankin gaba daya, inda ya ci gaba da shawagi a yankin har zuwa safiyar ranar 6 ga Yuli, 2022.

“Bayan ganin yadda ‘yan ta’adda kusan 18 suka taru a wurin, jirgin ya kai hari. An yi nasarar kashe da dama daga cikinsu.

“Sakamakon da aka samu ya nuna cewa harin ya yi daidai kuma an yi nasara.

“Har yanzu ana ci gaba da kokarin gano tare da lalata sauran maboyar ‘yan ta’addan da ke cikin Katsina da kuma Arewa maso Yamma baki daya,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 
Manyan Labarai

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025
Next Post
Buhari Ya Fusata Game Da Harin Gidan Yarin Kuje, Yana Bukatar Amsa

Buhari Ya Fusata Game Da Harin Gidan Yarin Kuje, Yana Bukatar Amsa

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025
An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.