ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jiragen Yaki Sun Kashe ‘Yan Bindiga 42 A Katsina

by Sadiq
4 years ago
Jiragen Yaki

Rundunar Sojin Sama ta Operation Hadarin Daji ta kashe ‘yan ta’adda 42 a kusa da kauyukan Zakka da Umadan a karamar hukumar Safana ta Jihar Katsina.

A cewar majiyar sojin, wani jirgin saman yakin Nijeriya a yayin da ya ke shawagi a sama, ya samu bayanan sirrin ganin ‘yan ta’adda a tsakanin kauyukan Zakka da Umadan.

  • Harin Kuje: Buhari Ya Nuna Rashin Jin Dadinsa Kan Tsaron Kasar Nan
  • Da Dumi-Dumi: Mune Muka Kai Hari Gidan Yarin Kuje – ISWAP

Wannan dai na zuwa ne a yayin da ‘yan ta’addan suka kai hari ofishin ‘yan sanda da ke kauyen Zakka a baya-bayan da ke Dutsenma tare da harbe wani jami’in ‘yan sanda har lahira.

ADVERTISEMENT

A ranar Talata ne ‘yan ta’addan suka kai hari kan ayarin motocin shugaban kasa a jihar.

Wani babban jami’in rundunar sojin sama, ya ce an gano ‘yan ta’adda a wani kauye mai tazarar kilomita 7.1 daga yammacin garin Safana da kuma yammacin kauyen Yartuda.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ya kara da cewa an kuma ga wasu mutanen garin na guduwa daga kauyen saboda ‘yan ta’addan sun yi awon gaba da wasu daga cikin mutanen garin.

“An yi sa’a, kamar yadda aka yi tsammani, daga baya an ga wadanda aka yi garkuwa da su suna tserewa bayan nasarar da jirgin NAF ya samu na kashe maharan.

“Abin da ya biyo bayan harin ta sama shi ne an ga wasu daga cikin mutanen kauyen da suka watse a lokacin da ‘yan ta’addan suka fara mamaye kauyen suna dawowa.

“Mutanen kauyen sun kuma tabbatar da cewa an kawar da ‘yan ta’adda sama da 24 a hare-hare da aka kai ta sama,” in ji majiyar.

“Saboda haka, an aike da wani jirgin yakin zuwa yankin gaba daya, inda ya ci gaba da shawagi a yankin har zuwa safiyar ranar 6 ga Yuli, 2022.

“Bayan ganin yadda ‘yan ta’adda kusan 18 suka taru a wurin, jirgin ya kai hari. An yi nasarar kashe da dama daga cikinsu.

“Sakamakon da aka samu ya nuna cewa harin ya yi daidai kuma an yi nasara.

“Har yanzu ana ci gaba da kokarin gano tare da lalata sauran maboyar ‘yan ta’addan da ke cikin Katsina da kuma Arewa maso Yamma baki daya,” in ji shi.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Buhari Ya Fusata Game Da Harin Gidan Yarin Kuje, Yana Bukatar Amsa

Buhari Ya Fusata Game Da Harin Gidan Yarin Kuje, Yana Bukatar Amsa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.