• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sharhi: Lokaci Ya Yi Da Tinubu Zai Fuskanci Matsalolin Nijeriya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Sharhi: Lokaci Ya Yi Da Tinubu Zai Fuskanci Matsalolin Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bayan kotun koli ta tabbatar da nasarar zaben Bola Ahmed Tinubu a matsayin zababben shugaban Nijeriya, yanzu lokaci ya yi da shugaban kasar zai mayar da hankali wajen inganta gwamnatinsa ta yadda zai iya tunkarar matsaloli da ke fuskantar Nijeriya kamar yadda ya yi alkawari a lokacin yakin neman zabe.

Kwanaki sama da 50 kenan da kotun sauraron karar zaben shugaban kasa ta goyi bayan hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) a kan ayyana dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu shi ya yi nasara a zaben da ya gudana a ranar 25 ga Fabrairun 2023. Yayin da ita ma kotun koli a ranar Alhamis, 26 ga Oktoba ta tabbatar da wannan hukunci.

  • Baje Kolin CIIE Na Kara Jan Hankalin Sassa Kasa Da Kasa
  • Sojoji Sun Kashe Kasurgumin Kwamandan ‘Yan Bindiga A Kebbi

A hukuncin, alkalan kotun kolin su bakwai sun bayyana cewa wadanda suka shigar da kara sun gaza kawo kararan hujjoji da za su kore nasarar da Tinubu ya samu a zaben shugaban kasar.

Bayan watsi da kararrakin guda biyu da ‘yan takarar jam’iyyar PDP, Alhaji Atiku Abubakar da na LP, Mista Peter Obi suka shigar, kotun kolin ta tabbatar da hukuncin da kotun sauraron karar zaben shugaban kasa ta yanke a ranar 6 ga watan Satumba, inda ta tabbatar da ayyana Tinubu a matsayin shugaban Nijeriya.

Hukuncin da kotun koli ta yanke, ba wai kawai ya kawo karshen duk wasu kararraki da suka shafi zaben shugaban kasa ba, har ma da tabbatar da aikin shugaban kasa na tsawon shekaru hudu masu zuwa.

Labarai Masu Nasaba

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Ayyukan sun hada da samar da ingantacciyar shugabanci, samar da ingantacciyar rayuwa ga ‘yan Nijeriya wanda hakan ta sa aka cire tallafin man fetur da kuma dawo da darajar naira, wanda gwamnatin Tinubu ta fara tun daga farkon lamari.

Sai dai babban kalubalen da ke fuskantar ‘yan Nijeriya sun hada da rashin zaman lafiya, rashin samun ci gaba, ayyukan ‘yan bindiga da kuma cin hanci da rashawa.

Kamar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari da ke cewa, “idan ba mu yaki ci hanci da rashawa ba, to zai kashe mu “. Cin hanci da rashawa kamar wutar daji ce da ke cin zukatan ‘yan Nijeriya. Babu wani bangare na rayuwar ‘yan Nijeriya da cin hanci bai dabaibaye ba.

Domin haka, dole ne gwamnatin Tinubu ta mayar da hankali wajen karfafa yaki da cin hanci da rashawa. A lokacin yakin neman zabe, Tinubu ya yi wa ‘yan Nijeriya alkawarin sake farfado da darajar Nijeriya.

Lallai idan har ‘yan Nijeriya za su ga sauyi, to dole ne Tinubu ya tashi tsaye wajen inganta gwamnatinsa da kuma yaki da cin hanci da rashawa a kowani bangare. Mafi yawancin mutane sun yi kara ga shugaban kasa ya yi kokarin gudanar da shugabanci nagari ta yadda zai iya farfado da darajar Nijeriya a idon duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Matar Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar Da Bada Tallafin N50,000 Ga Mata Dubu 4 A Gusau

Next Post

Tsaro: Bai Wa Al’umma Bindiga Su Kare Kai Ya Saba Wa Doka – Shugaban NCM

Related

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

1 day ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

2 days ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

2 days ago
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

1 week ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

1 week ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

1 week ago
Next Post
Tsaro: Bai Wa Al’umma Bindiga Su Kare Kai Ya Saba Wa Doka – Shugaban NCM

Tsaro: Bai Wa Al'umma Bindiga Su Kare Kai Ya Saba Wa Doka – Shugaban NCM

LABARAI MASU NASABA

Kawu Sumaila Ya Yabi Gwamnatin Kano Kan Goyon Bayan Kirkiro Sabuwar Jihar Tiga

Kawu Sumaila Ya Yabi Gwamnatin Kano Kan Goyon Bayan Kirkiro Sabuwar Jihar Tiga

July 13, 2025
Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

Wasu Ma’aikatan Fadar Kano Sun Maka Sarki Sanusi Gaban Kotu

July 13, 2025
Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

Cote d’Iboire Ta Amince Da Kafa Bankin Makamashi Na Afirka

July 13, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

‘Mutum Miliyan 14 Na Iya Mutuwa Nan Da 2030 Saboda Janye Tallafin Trump’

July 13, 2025
Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

Abubuwa 5 da Ya Kamata Ku Sani Game da Wasan Ƙarshe Tsakanin Chelsea Da PSG

July 13, 2025
Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

Abubuwa 10 Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Peter Rufai, Fitaccen Golan Nijeriya

July 13, 2025
Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

Dan Gidan Ancelloti Ya Zama Sabon Kocin Botafago FC

July 13, 2025
NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.