• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Ziyarci Hukumar ‘Yan Gudun Hijira, Ya Karbo Wa Zamfara Kayan Tallafi

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Gwamna Lawal Ya Ziyarci Hukumar ‘Yan Gudun Hijira, Ya Karbo Wa Zamfara Kayan Tallafi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara, ya karbo wa jihar kayan tallafi domin raba wa wadanda rikicin ‘yan bindiga ya shafa a jihar.

Gwamnan ya ziyarci hukumar kula da ‘yan gudun hijira da bakin haure ne a ranar Alhamis.

  • Majalisar Wakilai Ta Nemi A Cefanar Da Sufurin Jirgin Kasa
  • Dakarun Tsaron Hadin Guiwa Sun Dakile Harin ‘Yan Ta’adda Da Cafke Mutum 2 A Kano

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris ya fitar, ta ce sun kai ziyarar ne domin fadakarwa, duba da irin rawar da hukumar ke takawa wajen bayar da agaji ga wadanda lamarin ya shafa.

A cewarsa, Gwamnan ya samu tarba daga Tijjani Aliyu Ahmed, kwamishinan tarayya na hukumar kula da ‘yan gudun hijira da bakin haure.

Ya ce: “Makasudin ziyarar Gwamna Lawal ga Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijira ta Kasa ita ce duba karin hanyoyin da za a taimaka wa wadanda harin ‘yan fashin daji suka shafa a Jihar Zamfara.

Labarai Masu Nasaba

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

“A yayin ziyarar, Gwamna Lawal ya roki hukumar da ta bai wa Zamfara fifiko saboda rashin tsaro da ake fama da shi da kuma bukatar agaji.

“Gwamnan ya jaddada bukatar hadin gwiwa wajen rage wa ’yan gudun hijira radadin yanayin da suke ciki su sama da 2000 a Zamfara.”

A lokacin da yake jawabi, kwamishinan hukumar, Tijjani Aliyu Ahmed, ya jaddada aniyar hukumar na ci gaba da tallafa wa jama’ar jihar Zamfara da sauran jihohin da ke fama da matsalar rashin tsaro.

Kwamishinan ya yaba wa Gwamnan Zamfara bisa kasancewarsa shugaba na farko da ya ziyarci hukumar tun bayan hawansa mulki.

“Abin alfahari ne da kuka ziyarce mu, wanda hakan ke nuna jajircewarku wajen kyautata rayuwar jama’arku. Mun saurari bukatarku. Don haka hukumar za ta tabbatar da cewar ta yi abin da ya dace.”

Hukumar ta bayar da tallafi ga jihar Zamfara a wani bangare na aikin agajin gaggawa wanda ya hada da buhunan shinkafa, katon din taliya, kayan aikin noma na manoma, kwamfutoci, injin dinki na masana’antu, injinan yanka katako, litattafai da sauran abubuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Wakilai Ta Nemi A Cefanar Da Sufurin Jirgin Kasa

Next Post

Yadda Matata Ta Rasu A Kokarin Kare Mutuncinta Daga Masu Garkuwa – Yusuf

Related

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

1 hour ago
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro
Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

2 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

3 hours ago
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa
Manyan Labarai

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

3 hours ago
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta
Manyan Labarai

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

5 hours ago
Next Post
Yadda Matata Ta Rasu A Kokarin Kare Mutuncinta Daga Masu Garkuwa – Yusuf

Yadda Matata Ta Rasu A Kokarin Kare Mutuncinta Daga Masu Garkuwa – Yusuf

LABARAI MASU NASABA

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.