• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gudanar Da Gasar Adabi karo Na Uku Don Bunƙasa Ilimin ‘Ya’ya Mata A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Labarai
0
Yadda Aka Gudanar Da Gasar Adabi karo Na Uku Don Bunƙasa Ilimin ‘Ya’ya Mata A Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An gudanar da gasar adabin ne don bunƙasa ilimin ‘ya’ya mata karo na uku mai taken ‘Fatima Dikko Raɗɗa girls child education summit and literacy contest’

Ita dai wannan gasa an samar da ita ce da nufin karfafa guiwar ‘ya’ya mata musamman abin da ya shafi karatunsu tun daga matakin firamare har zuwa jami’a ta yadda za su riƙa samun wakilci a fannonin rayuwa.

  • ‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina
  • Gwamna Dikko Ya Amince Da Bude Asusun Bai-daya A Jihar Katsina

A karo na uku na wannan gasa, an zakulo ɗalibai daga ɓangarori huɗu da suka haɗa da ƙanana da manyan makarantun sakandire da masu karatu a matakin digiri na daya da na biyu domin fafatawa a wannan gasa wanda kungiyar ‘read Right Multipurpose education society’ suka saba shiryawa.

Ɗaliban da suka fafata a cikin wannan gasa su kimanin ɗalibai 41 daga ƙaramar sakandire sai kuma ɗalibai 54 daga babbar sakandire, sai ɗalibai 19 masu karatun digiri da kuma mutum biyu masu karatun digiri na biyu.

Daga cikin mahimman batutuwa da aka tattauna a wannan gasar ta bana sun haɗa da batun samar da tsaftattaccen ruwan sha da irin rawar da mata ke takawa wajan samar da tsaftataccen ruwan sha da batun ciwon daji ‘cancer’ da dai sauransu

Labarai Masu Nasaba

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Haka kuma kowanne rukuni an fitar da na ɗaya zuwa na uku, inda aka ba su kyaututtuka da kuɗaɗe domin ƙara masu ƙwarin guiwa musamman abin da ya shafi karatunsu.

Tun da farko shugaban kungiyar ‘Read Right Multipurpose education society’ Aliyu Nasir Ƙanƙara ya bayyana wasu ayyukan wannan kungiyar inda ya ce, an samu gagarumar nasara a cikin wannan shekarar ta 2023.

“Mun ƙaddamar da rabon littattafai a ƙaramar hukumar Musawa da Dabai a ƙaramar hukumar Danja, mun yi gangamin wayar da kai kan sha’anin shugabanci da kuma bayar da abinci a lokacin watan Ramadan da ya gabata”. Inji shi

Ya ƙara da cewa a shirinsu na a koma makaranta ”Back to School Campaign’ sun samu nasarar mayar da yaran da ba sa zuwa makaranta 7,500, sannan sun yi taron wayar da kai dangane da matsalar rikice-rikecen cikin gida da sauran batutuwa da suka shafi al’umma.

Ita ma a nata jawabin kwamishiniyar ilimi a matakin farko, Hajiya Hadiza Yar’adua, ta yi bayanin cewa irin wannan gasa na nuna irin yadda aka nuna kulawa ga ilimin ‘ya ‘ya mata

Kwamishinan ta ce ko ba komi l, an sanar da wata sabuwar hanya ta karfafa guiwar ‘ya’ya mata wanda hakan ba zai sa a bar su a baya ba ta bangarori da dama.

“Yanzu muryoyin ‘ya ‘ya mata za su fara yin amo na gaskiya, musamman abubuwan da suka shafi ilimi na zamani da kuma na addini” inji ta.

Kwamishiniyar harkokin mata ta jihar Katsina, Hajiya Zainab Musa Musawa, ta nuna mahimmancin yin ilimin ga ‘ya’ya mata musamman a wannan lokaci da ake da ƙalubale kala-kala na rayuwa.

A jawabinta mai ɗakin gwamnan jihar Katsina, Hajiya Fatima Dikko Raɗɗa, ta nuna farin cikinta kan yadda ɗalibai suka nuna ƙwazo da jajircewa a lokacin wannan gasa da ta gudana.

Hajiya Fatima Dikko Raɗɗa ta ce, haƙiƙa sun zama abin alfahari ga al’ummar jihar Katsina ta yadda da irin haka ne za su canza alƙiblar ilimi musamman na ‘ya’ya mata a jihar Katsina da arewacin Nijeriya.

An kammala wannan gasa ta adabi da bunkasa ilimi ‘ya’ya mata da aka yi kwanaki biyu ana gudanarwa tare da raba kyaututtuka ga waɗanda suka samu nasarar lashe gasar a Katsina.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdabiGasaKatsina
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mutane 132 Sun Rasu A Girgizar Kasar Yankin Nepal

Next Post

Real Madrid Ta Dawo Matsayi Na 2 A Laliga Bayan Yin Canjaras Da Vallecano

Related

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?
Manyan Labarai

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

36 minutes ago
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

48 minutes ago
gasa
Labarai

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

3 hours ago
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki
Labarai

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

4 hours ago
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

5 hours ago
gasa
Labarai

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

8 hours ago
Next Post
Real Madrid Ta Dawo Matsayi Na 2 A Laliga Bayan Yin Canjaras Da Vallecano

Real Madrid Ta Dawo Matsayi Na 2 A Laliga Bayan Yin Canjaras Da Vallecano

LABARAI MASU NASABA

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

Dokar Hana Ƙara Kuɗin Makaranta A Kaduna: Alheri Ce Ko Barazana Ga Makarantu Masu Zaman Kansu?

September 19, 2025
Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

Tinubu Ya Ziyarci Iyalan Buhari A Jihar Kaduna

September 19, 2025
Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Bunkasa Ci Gaban Mata

September 19, 2025
Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

Ofishin Yada Labarai Na Majalisar Gudanarwar Kasar Sin Ya Fitar Da Takardar Bayani Mai Taken “Nasarar Aiwatar Da Manufar JKS A Xinjiang A Sabon Zamani”

September 19, 2025
gasa

Tarihin Ahmadu Bello Sardaunan Sakkwato Firimiyan Arewa

September 19, 2025
Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

Xi Jinping Ya Aika Wasikar Taya Murnar Cika Shekaru 100 Da Kafuwar Jam’iyyar Zhigong Ta Sin

September 19, 2025
An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

An Dakatar Da Shugabannin Makarantun Sakandire 6 A Sakkwato Kan Rashin Bin Dokokin Aiki

September 19, 2025
Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
gasa

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

September 19, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.