ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Aka Gudanar Da Gasar Adabi karo Na Uku Don Bunƙasa Ilimin ‘Ya’ya Mata A Katsina

by El-Zaharadeen Umar
3 years ago
gasa

An gudanar da gasar adabin ne don bunƙasa ilimin ‘ya’ya mata karo na uku mai taken ‘Fatima Dikko Raɗɗa girls child education summit and literacy contest’

Ita dai wannan gasa an samar da ita ce da nufin karfafa guiwar ‘ya’ya mata musamman abin da ya shafi karatunsu tun daga matakin firamare har zuwa jami’a ta yadda za su riƙa samun wakilci a fannonin rayuwa.

  • ‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina
  • Gwamna Dikko Ya Amince Da Bude Asusun Bai-daya A Jihar Katsina

A karo na uku na wannan gasa, an zakulo ɗalibai daga ɓangarori huɗu da suka haɗa da ƙanana da manyan makarantun sakandire da masu karatu a matakin digiri na daya da na biyu domin fafatawa a wannan gasa wanda kungiyar ‘read Right Multipurpose education society’ suka saba shiryawa.

ADVERTISEMENT

Ɗaliban da suka fafata a cikin wannan gasa su kimanin ɗalibai 41 daga ƙaramar sakandire sai kuma ɗalibai 54 daga babbar sakandire, sai ɗalibai 19 masu karatun digiri da kuma mutum biyu masu karatun digiri na biyu.

Daga cikin mahimman batutuwa da aka tattauna a wannan gasar ta bana sun haɗa da batun samar da tsaftattaccen ruwan sha da irin rawar da mata ke takawa wajan samar da tsaftataccen ruwan sha da batun ciwon daji ‘cancer’ da dai sauransu

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Haka kuma kowanne rukuni an fitar da na ɗaya zuwa na uku, inda aka ba su kyaututtuka da kuɗaɗe domin ƙara masu ƙwarin guiwa musamman abin da ya shafi karatunsu.

Tun da farko shugaban kungiyar ‘Read Right Multipurpose education society’ Aliyu Nasir Ƙanƙara ya bayyana wasu ayyukan wannan kungiyar inda ya ce, an samu gagarumar nasara a cikin wannan shekarar ta 2023.

“Mun ƙaddamar da rabon littattafai a ƙaramar hukumar Musawa da Dabai a ƙaramar hukumar Danja, mun yi gangamin wayar da kai kan sha’anin shugabanci da kuma bayar da abinci a lokacin watan Ramadan da ya gabata”. Inji shi

Ya ƙara da cewa a shirinsu na a koma makaranta ”Back to School Campaign’ sun samu nasarar mayar da yaran da ba sa zuwa makaranta 7,500, sannan sun yi taron wayar da kai dangane da matsalar rikice-rikecen cikin gida da sauran batutuwa da suka shafi al’umma.

Ita ma a nata jawabin kwamishiniyar ilimi a matakin farko, Hajiya Hadiza Yar’adua, ta yi bayanin cewa irin wannan gasa na nuna irin yadda aka nuna kulawa ga ilimin ‘ya ‘ya mata

Kwamishinan ta ce ko ba komi l, an sanar da wata sabuwar hanya ta karfafa guiwar ‘ya’ya mata wanda hakan ba zai sa a bar su a baya ba ta bangarori da dama.

“Yanzu muryoyin ‘ya ‘ya mata za su fara yin amo na gaskiya, musamman abubuwan da suka shafi ilimi na zamani da kuma na addini” inji ta.

Kwamishiniyar harkokin mata ta jihar Katsina, Hajiya Zainab Musa Musawa, ta nuna mahimmancin yin ilimin ga ‘ya’ya mata musamman a wannan lokaci da ake da ƙalubale kala-kala na rayuwa.

A jawabinta mai ɗakin gwamnan jihar Katsina, Hajiya Fatima Dikko Raɗɗa, ta nuna farin cikinta kan yadda ɗalibai suka nuna ƙwazo da jajircewa a lokacin wannan gasa da ta gudana.

Hajiya Fatima Dikko Raɗɗa ta ce, haƙiƙa sun zama abin alfahari ga al’ummar jihar Katsina ta yadda da irin haka ne za su canza alƙiblar ilimi musamman na ‘ya’ya mata a jihar Katsina da arewacin Nijeriya.

An kammala wannan gasa ta adabi da bunkasa ilimi ‘ya’ya mata da aka yi kwanaki biyu ana gudanarwa tare da raba kyaututtuka ga waɗanda suka samu nasarar lashe gasar a Katsina.

gasa
El-Zaharadeen Umar
+ postsBio
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Mutum 1,000 Daga Jam’iyyar ADC Sun Koma PDP A Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Tinubu Ya Amince Da Ɗaukar Ma’aikatan Gandun Daji 1,000 Domin Matsalolin Tsaro A Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Matsalar Tsaro:Yadda Sabbin Matakan Gwamnati Ke Shafar Walwalar Al’ummar Jihar Katsina
  • El-Zaharadeen Umar
    https://hausa.leadership.ng/author/el-zaharadeen-umar/
    Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Real Madrid Ta Dawo Matsayi Na 2 A Laliga Bayan Yin Canjaras Da Vallecano

Real Madrid Ta Dawo Matsayi Na 2 A Laliga Bayan Yin Canjaras Da Vallecano

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.