• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Baje Kolin CIIE: Kasashen Afirka Kar Ku Yarda A Bar Ku A Baya

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Bikin Baje Kolin CIIE: Kasashen Afirka Kar Ku Yarda A Bar Ku A Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin na duniya (CIIE) ya nuna kudurin kasar Sin na hada kan duniya domin cin gajiyar juna ta fuskar tattalin arziki har ma da zamantakewa.

A karon farko da na samu labarin bikin, na yi tunanin akwai yiwuwar za a bar ’yan kasuwarmu na Afirka da dama a baya wurin shiga a dama da su, saboda rashin karfin jari irin na takwarorinsu na sauran duniya.

  • Xi Zai Gana Da Biden Tare Da Halartar Taron Shugabannin Tattalin Arzikin APEC
  • Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

Amma bisa bayanan da na ji daga cibiyar baje kolin, a ziyararmu ta aiki a 2018 a Shanghai, shugabannin shiryawa sun ce, baje kolin na CIIE ya tsara taimakawa kasashe masu rauni wajen ba su matsugunai domin baje kolinsu ba tare da biyan kudi ba har ma da wani tallafi da zai taimaka wa kayayyakinsu su samu damar shiga kasuwar kasar Sin.

Wannan tsari ya haifar da da mai ido, domin ko a bana, daga kasar Zimbabwe kawai, fiye da kamfanoni da kungiyoyi 15 da suka kware a fannin fasahar zane, da sarrafa kayayyakin fata, da harkokin sadarwa, da kuma sayar da ma’adanai, suke halartar bikin baje kolin.

Haka nan daga Nijeriya da Afirka ta Kudu da sauran kasashe duk suna can ana damawa da su a bikin baje kolin na bana karo na 6 a birnin Shanghai.

Labarai Masu Nasaba

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Baje kolin na CIIE, karin dama ce ga Nijeriya ta samun cinikin kayan da take fitarwa zuwa Sin kamar su kwarar manja, ridi, ‘ya’yan itace, hatsi har ma da waken soya wanda cinikayyarsu sun kai Dalar Amurka miliyan 140.88 a shekarar 2021, bisa bayanan cibiyar cinikayya ta COMTRADE ta Majalisar Dinkin Duniya.

Shugaban Tsangayar Aikin Gona da Raya Karkara ta ARMTI da ke Nijeriya, Dr. Olufemi Oladunni, ya bayyana cewa, “akwai damammaki da yawa da manoman Nijeriya za su ci gajiya a kasuwanni na kasashen duniya bisa cudanya da ‘yan kasuwa na waje, manoman za su samu dabarun inganta noma, da yadda za su rika sarrafa amfanin gona bayan girbi da kuma fitarwa waje.”
Har ila yau, manajan daraktar kamfanin sarrafa kayan fata na Samuneti dake Zimbabwe, Tsitsi Chirova, ta ce baje kolin CIIE fage ne da suke samun damar fadada hadin gwiwa da kara fahimtar ire-iren kayayyakin da za su rika sarrafawa. “Daga shigar da muka yi a baya, mun sami damar habaka tallace-tallacenmu, da kuma samun shawarwari daga abokan cinikinmu don habaka abubuwan da muke samarwa. Don haka idan muka halarci bikin baje kolin na kasar Sin, na yi imani hakan zai tallata kamfaninmu da gaske, kuma bayan mun dawo gida, mun yi imanin za mu samu karin kwastomomi,” in ji ta.

Shi ma wani mai sassaka dake birnin Harare, Richard Mudinzva, da ya sha alwashin halartar bikin karo na 6, ya ce, akwai abokan ciniki da yawa a kasuwar kasar Sin dake sha’awar kayayyakin Afirka. Alkaluman da ofishin jakadancin kasar Sin dake Zimbabwe ya fitar sun nuna cewa, cinikayyar bangarorin biyu ta karu da kashi 39.4 bisa dari, zuwa dala biliyan 2.43 daga Janairu zuwa Satumbar 2023, wanda ya zarce adadin cinikin da aka samu a shekarar 2022.

Kasar Guinea-Bissau, mafi noman kashu a duniya, ta ci gajiyar bikin baje kolin a bara, yayin da aka ware mata matsugunin kamfanoninta suka baje kolinsu na kashu. Kamar yadda jakadan kasar a Sin, Antonio Serifo Embalo ya bayyana, sakamakon halartar bikin baje kolin na bara, ’yan kasuwa da dama sun nuna muradinsu a kan bangaren kashu na kasar. Wasu ma tuni har sun tsara yadda za su zuba jari a kasar.
A nashi bangaren, mataimakin shugaban Afirka ta Kudu, Paul Mashatile, ya yaba wa kasar Sin bisa yadda take kara bude kofofinta na kasuwanci musamman ga kasashen Afirka. Yana mai cewar, bikin baje kolin ya kara fadada dama ga kamfanoni na duniya wajen bunkasa hulda da abokan ciniki.

Sama da kamfanoni 1,500 daga kasashen dake cikin shawarar “ziri daya da hanya daya” ke baje kolin hajojinsu a bikin karo na shida.

Ana sa rai, cinikayyar shigo da kaya na kasar Sin su zarce dala tiriliyan 17 nan da shekara 5 masu zuwa, don haka nake cewa, kasashen Afirka kar ku yarda a bar ku a baya wajen cin gajiyar hakan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Game Da Manufofin JKS Na Jagorancin Yankin Xizang A Sabon Zamani

Next Post

Bankin TAJ Ya Sake Lashe Kyautar Gwarzon Bankin Musulunci Na Bana

Related

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

3 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

5 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

6 hours ago
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

22 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

22 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

1 day ago
Next Post
Taj

Bankin TAJ Ya Sake Lashe Kyautar Gwarzon Bankin Musulunci Na Bana

LABARAI MASU NASABA

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
CIIE

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.