• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kasashen Afirka Na Cin Gajiyar Aikin Zamanintar Da Aikin Gona Na Sin

by CGTN Hausa
2 years ago
Gona

Innocent Mojidi dan kasar Najeriya ne mai shekaru 35 da haifuwa, ya taba zuwa kasar Sin sau biyu don samun horo a fannin aikin gona, yauzu yana noman shimkafa da masara a gonakinsa dake karkarar birnin Abuja hedkwatar Najeriya. Saboda kwarewar da ya samu, ya zama masanin aikin gona a garinsu. ‘Yan Afrika da dama ne kamar Innocent Mojidi suka zo kasar Sin don koyon dabarun aikin noma na zamani, matakin da ya taimaka musu wajen tinkarar matsalar karancin isasshen hatsi.

A cikin shekaru 10 da suka gabata bayan Sin da Afrika suka yi hadin gwiwa a fannin aikin noma, Sin ta kulla yarjeniyoyi 34 da kasashen Afrika da AU da AGRA a wannan bangare, da kuma yin mu’ammala kan samar da isasshen hatsi da rage talauci da tinkarar sauyin yanayi da sauransu. Ban da wannan kuma, ma’aikatar aikin noma da raya kauyuka ta kasar sin ta tura masananta fiye da 400 zuwa kasashen Afrika tare da horar da ‘yan Afrika fiye da dubu 10.

  • Yanzu-yanzu: Kotun Daukaka Kara Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Zaben Gwamnan Kano Gobe A Abuja
  • Xi Jinping Ya Fara Ganawa Da Joe Biden

Ban da samar da dabaru na kimiyya da fasaha, Sin ta taimakawa kasashen Afrika wajen gina wasu manyan ababen more rayuwa a wannan fanni. Gwamnatin Sin ta tallafawa Najeriya wajen gina cibiyar raya aikin gona ta gwaji a Abuja kyauta, wannan cibiyar ta fitar da wani nau’in irin shimkafa samfurin Gawal R1, kuma an yi shekaru 5 ana shuka wannan iri a Najeriya, wanda ya samar da karin shinkafa tan miliyan 2, inda manoma fiye da dubu 200 suka ci gajiya. A cikin shekaru 10 da suka gabata, Sin ta taimakawa kasashen Afrika wajen gina cibiyoyin gwaji a fannin aikin noma 24, inda aka gabatar tare da yayata fasahohi fiye da 300 a wuraren, yawan karuwar hatsi da aka samu ya kai kashi 30% zuwa 60%, manoma kimanin miliyan 1 sun ci gajiyar wadannan fasahohi.

Yanzu, gwamnatin Sin na kara karfafa hadin gwiwa da kasashen Afrika a wannan fanni, kuma ta gudanar da dandalin hadin kan Sin da Afrika a fannin aikin gona karo na 2 a birnin Sanya na lardin Hainan dake kudancin kasar Sin daga ran 13 zuwa 15. Dandalin na da zummar habaka hadin kan bangarorin biyu, ta yadda za a kara inganta ayyukan gona a kasashen Afrika, tare da cimma muradun samun ci gaba nan da shekara ta 2030 a wannan bangare a kasashen Afrika.

Ayyukan hadin kai a bangaren aikin noma karkashin shirin hadin kan kasashe masu tasowa da shawarar “ziri daya da hanya daya” sun samarwa kasashe masu tasowa musamman ma kasashen Afrika tallafin manyan ababen more rayuwa a fannin aikin noma da kudade da fasahohi da hatsi da sauransu, matakan da za su taimaka musu wajen samun bunkasuwa da dogara da karfin kansu. Labarin Mojidi da cibiyar gwaji ta fasahohin aikin noma dake Abuja sun zama misali ta fuskar hadin kan Sin da Afrika. Ana sa ran cewa, a cikin shekaru 10 masu zuwa, bangarorin biyu za su samu karin ci gaba a wannan fanni. (Mai zana da rubuta: MINA)

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona
Daga Birnin Sin

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Next Post
Sin Da Afirka Na Da Makoma Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwar Aikin Gona

Sin Da Afirka Na Da Makoma Mai Kyau A Fannin Hadin Gwiwar Aikin Gona

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

An Kashe Ɗan Sanda Da Ɗan Hakimi A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Gombe

October 29, 2025
Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Siyasa Kan Tayar Da Hankali A Zaɓen Anambra

October 29, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

Ba Matakan Tinubu Ne Suka Karyar Da Farashin Kayan Abinci Ba – ADC

October 29, 2025
‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

‘Yan Ta’adda Sun Yi Barazanar Sanya Wa Majalisa Bam – Ɗan Majalisa

October 29, 2025
Sanusi Ga ‘Yan Nijeriya: Ku Dora Wa Buhari Alhakin Matsatsin Tattalin Arziki Ba Tinubu Ba

Tsoron Boko Haram Ne Ya Sa Jonathan Ya Fasa Cire Tallafin Man Fetur – Sanusi II

October 29, 2025
Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.