• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

by Bello Hamza
2 years ago
in Rahotonni
0
Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

A kwanaki ne aka kaddamar da babban masallacin Juma’a na unguwar Adogba da ke garin Ibadan wanda Mai Alfarma Sultan na Sakkwato Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar ya jagorancin budewa, Gwamnan Jihar Oyo ‘Seyi Makinde ya gina, bayan da aka rusa tsohuwar masallacin a shekarar 2019 don sabunta ta don samar da karin fahimtar juna da kuma kawar da bambancin kabilanci da na addini.

A lokacin da gwmanatin jihar Oyo ta rusa masallacin Adogba wanda ake kuma kira da ‘Organisation of Tadhamunul Muslimeen Moskue’, da ke Adogba, a kan hanyar Iwo a cikin garin Ibadan a shekarar 2019 don samar da babbar tashar mota ta ‘Iwo Road’, da yawan al’umma ba su natsu da yadda aka rusa masallacin ba, amma tabbacin da gwamnan Jihar Oyo, ‘Seyi Makinde ya bayar na cewa, za a gina sabon masallaci ya sa al’umma Musulmi duniya suka natsu tare da jin dadin lamarin.

  • Zargin Baɗala: Hisba Ta Kama Mata Da Maza A Zamfara
  • Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Na Wucin Gadi Tsakanin Palasdinu Da Isra’ila 

Shekara 4 bayan rusau da aka yi a daidai ranar 16 ga watan Nuwamba 2023 Makinde ya cika alkawarin da ya yi na sake gina babban masallacin Adogba daga cikin kudi mallakin kansa, a inda shugaban majalisar koli ta addnin musulunci kuma Sultan na Sakkwato, Mai Martaba Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, tare da rakiyar Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero da Gwamna ‘Seyi Makinde suka jagoranci kaddamarwa.

Kasancewar Shugaban Al’umma Musulmun Nijeriya, Sultan Abubakar da mai martaba Sarkin Kano da kuma wasu manyan jagororin Musulmi a Nijeriya ya kara bayyana bukatar karfafa fahimtar juna a bangaren addini da kabilanci, duk kuwa da matsalolin da Nijeriya ke fuskanta.

A jawabinsa, Gwamna Makinde ya yaba wa al’ummar Musulmin Jihar Oyo a kan goyon bayan da suka bashi a zaben gwamnan da aka gudanar ranar 8 ga watan Maris 2023, ya kuma kara jaddada kudirinsa na gudanar da mulkin jihar tare da yin adalci da dukkan ma’abuta addinan da ke jihar.

Makinde ya kuma bayyana cewa, a lokacn da aka yanke shawarar rusa babban masallacin Adogba da wani coci da suke a kan inda gwamnantin jihar ta ke son gina babban tashar mota, an samu rashin jituwa daga bangaren al’umma muslmi, “Domin kuwa wasu na ganin lamarin a mastayin kamar an nuna banbanci”.

Ya kuma ce, “Na je na yi sallah tare da al’umma a masallacin, na yi musu bayanin cewa, masallacin tare da wani coci ne za a rusa saboda mun riga mun shirya gudanar da aikin babbar tashar mota, saboda muhimmancinta ga al’ummar jihar.

“Na fahimamci akwai rashin fahimma a tsakanin al’umma da gwamnati don ko kafin in kammala jawabi na har wasu sun fara gunaguni.

“Amma bayan da na yi jawabi a masallacin a ranar, sai na ga kusan kashi 90 na mutanen sun yarda da magana na, a kan haka kusan duk lokacin da na rasa kudin aikin masallacin (saboda na gina masallacin ne da kudin kashin kaina) sai in tuna kashi 90 na mutanen da suka yi Imani da abin da na fada musu, na cewa zan sake gida musu masallacin kamar yadda na yi alkawari, wannan yake karfafa ni”.

A nasa jawabin, mai martaba sarkin Musulmi kuma shugaban Majalisar Koli ta Addnin Musulunci, Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar, ya yaba wa Gwamna a kan yadda ya yi alkawarin gina masallaci ya kuma cika alkawarin.

Ya kara da cewa, “Idan ka kalli yadda masallacin yake a da da kuma yadda ya zama a halin yanzu ba abin da zaka ce sai mika godiya ga Allah a kan rayuwar ‘Seyi Makinde a kan tunaninsa da kuma yadda ya aiwatar da tunanin nasa.

“Mutane da dama na furta alkawarin yin wani abu amma in an zo aiwatarwa sai kaga sun samu matsalar cika alkawarin da suka yi,” in ji shi.

Sultan ya kuma lakaba wa gwamnan na jihar Oyo sunansa na ‘Sa’ad’ a kan yadda ya yi alkawari na gina dakin Allah ya kuma cika alkawarin, ya ce, sabon masallacin wanda ke da makarantar Islamiya zai taimaka wa al’umma wajen samun ilimi duniya da na gobe kiyama.

Sultan ya kuma kara jaddada cewa, “Ana kira na Sa’ad, amma a yau zan sanya maka suna Sa’ad. Muna godiya ga Allah da ya kawo mu garin Ibadan muka halarci wannan al’amari mai matukar muhimmanci.

“Kusan shekara uku da suka wuce na yi magana da gwamnan, ya gaya mani cewa yana gina masallaci a wani wuri mai muhimmanci a garin Ibadan, na ce masa na san wurin, ya kuma ce, ni zan kaddamar da masallacin in an gama na kuma amsa masa cewa, lallai zan zo don kaddamarwar da yardar Allah.

“Na zagaya yankin gaba daya, ina mai tabbatar muku da cewa, babu wani gini da ya kai wannan masallacin kyau. Duk ta inda ka fito zaka ga masallacin abin da ya kamata mu rinka yi kenan ga al’ummarmu. Ya kamata mu rika gina dakunan Allah masu kyau.

“Masallaci ba wai wurin bauta kadai ba ne, ya kuma kasance makaranta. A yanzu mun samu makarantar Islamiyya da kyakyawar masallaci, abu ne da zai karfafa mana neman ilimin duniya da na lahira. Saboda haka ya kamata mu yi amfani da makarantar wajen ilimantar da kanmu, ‘yanuwanmu da sauran al’umma don mu zauna lafiya da juna ba tare da wata matsala ba.

“Wannan tarihi ne mai kyau muna fatan a samu irinsa a wurare da dama, saboda haka muna godiya ga mai girma Gwamna,” in ji Sultan Abubakar.

Daga karshe ya kuma nemi a tabbatar da kula da masallacin yadda ya kamata.

A nasu martanin, wasu al’umma Musulmi sun yaba wa Gwamnan Jihar Oyo, ‘Seyi Makinde, sun kwatanta shi da mai cika alkawari, sun ce basu taba tunanin zai cika allawarin da ya yi a shekarar 2019 na gina masallacin ba.

Wani mai sallah a masallacin, mai suna Mista Olawole Abdulfatah, ya ce, bai taba tunanin gwamnan zai cika alkawarin da ya yi ba, don ya yi tunanin alkawari ne irin na ‘yan siyasa da basa cikawa.

Shi kuwa wani mai suna Mista Ganiyu Adebayo, ya ce, kasancewar Saltan da sauran manyan manyan al’umma musulmi daga arewacin kasar nan wata manuniya ce na cewa, ana mutunta Gwamna Makinde a sassan Nijeriya saboda karfafa fatimtar juna a tsakanin kabilu da addinai a Nijeriya.

Wasu da suka yi jawabi a wajen taron sun bayyana cewa, hadin kai da zaman lafiya a tsakanin al’umma yana da matukar muhimmanci ga ci gaban Nijeriya. Sun kuma yaba wa Gwamna Makinde a bisa hangen nesansa na karfafa hadin kai da zaman lafiya ba wai na Jihar Oyo ba harma da Nijeriya baki daya.

Wadanda suka halarci taron sun hada da tsohon shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayyar Nijeriya, Alhaji Yayale Ahmed, manyan malaman addinin musulunci da manyan ma’aikatan gwamnati.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Ta’asar Kungiyoyin Asiri Ke Neman Buwayar Jami’an Tsaro

Next Post

Bayan Wata 3: Har Yanzu Al’umma Na Cikin Kunci Duk Da Tallafin Naira Biliyan 180 Ga Jihohi

Related

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari
Rahotonni

Masana Sun Gano Dalilan Da Ke Taimaka Wa Ballewar Daurarru A Gidan Yari

3 days ago
Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa
Rahotonni

Dambarwar 2027 Da Kalubalen Da Ke Gaban Jam’iyyun Siyasa

1 week ago
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
Rahotonni

Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya

1 week ago
Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda
Rahotonni

Tinubu Ya Yi Wa Arewa Kokari Fiye Da Duk Wani Shugaba A Tarihin Nijeriya -Kwamared Dauda

2 weeks ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

1 month ago
Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
Rahotonni

Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki

1 month ago
Next Post
Bayan Wata 3: Har Yanzu Al’umma Na Cikin Kunci Duk Da Tallafin Naira Biliyan 180 Ga Jihohi

Bayan Wata 3: Har Yanzu Al’umma Na Cikin Kunci Duk Da Tallafin Naira Biliyan 180 Ga Jihohi

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.