• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Babban Masallacin Adogba: Sultan Da Makinde Sun Kafa Turbar Kawar Da Bambancin Kabilanci Da Na Addini A Nijeriya

by Bello Hamza
2 years ago
Adogba

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

A kwanaki ne aka kaddamar da babban masallacin Juma’a na unguwar Adogba da ke garin Ibadan wanda Mai Alfarma Sultan na Sakkwato Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar ya jagorancin budewa, Gwamnan Jihar Oyo ‘Seyi Makinde ya gina, bayan da aka rusa tsohuwar masallacin a shekarar 2019 don sabunta ta don samar da karin fahimtar juna da kuma kawar da bambancin kabilanci da na addini.

A lokacin da gwmanatin jihar Oyo ta rusa masallacin Adogba wanda ake kuma kira da ‘Organisation of Tadhamunul Muslimeen Moskue’, da ke Adogba, a kan hanyar Iwo a cikin garin Ibadan a shekarar 2019 don samar da babbar tashar mota ta ‘Iwo Road’, da yawan al’umma ba su natsu da yadda aka rusa masallacin ba, amma tabbacin da gwamnan Jihar Oyo, ‘Seyi Makinde ya bayar na cewa, za a gina sabon masallaci ya sa al’umma Musulmi duniya suka natsu tare da jin dadin lamarin.

  • Zargin Baɗala: Hisba Ta Kama Mata Da Maza A Zamfara
  • Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Wuta Na Wucin Gadi Tsakanin Palasdinu Da Isra’ila 

Shekara 4 bayan rusau da aka yi a daidai ranar 16 ga watan Nuwamba 2023 Makinde ya cika alkawarin da ya yi na sake gina babban masallacin Adogba daga cikin kudi mallakin kansa, a inda shugaban majalisar koli ta addnin musulunci kuma Sultan na Sakkwato, Mai Martaba Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar, tare da rakiyar Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero da Gwamna ‘Seyi Makinde suka jagoranci kaddamarwa.

Kasancewar Shugaban Al’umma Musulmun Nijeriya, Sultan Abubakar da mai martaba Sarkin Kano da kuma wasu manyan jagororin Musulmi a Nijeriya ya kara bayyana bukatar karfafa fahimtar juna a bangaren addini da kabilanci, duk kuwa da matsalolin da Nijeriya ke fuskanta.

A jawabinsa, Gwamna Makinde ya yaba wa al’ummar Musulmin Jihar Oyo a kan goyon bayan da suka bashi a zaben gwamnan da aka gudanar ranar 8 ga watan Maris 2023, ya kuma kara jaddada kudirinsa na gudanar da mulkin jihar tare da yin adalci da dukkan ma’abuta addinan da ke jihar.

Makinde ya kuma bayyana cewa, a lokacn da aka yanke shawarar rusa babban masallacin Adogba da wani coci da suke a kan inda gwamnantin jihar ta ke son gina babban tashar mota, an samu rashin jituwa daga bangaren al’umma muslmi, “Domin kuwa wasu na ganin lamarin a mastayin kamar an nuna banbanci”.

Ya kuma ce, “Na je na yi sallah tare da al’umma a masallacin, na yi musu bayanin cewa, masallacin tare da wani coci ne za a rusa saboda mun riga mun shirya gudanar da aikin babbar tashar mota, saboda muhimmancinta ga al’ummar jihar.

“Na fahimamci akwai rashin fahimma a tsakanin al’umma da gwamnati don ko kafin in kammala jawabi na har wasu sun fara gunaguni.

“Amma bayan da na yi jawabi a masallacin a ranar, sai na ga kusan kashi 90 na mutanen sun yarda da magana na, a kan haka kusan duk lokacin da na rasa kudin aikin masallacin (saboda na gina masallacin ne da kudin kashin kaina) sai in tuna kashi 90 na mutanen da suka yi Imani da abin da na fada musu, na cewa zan sake gida musu masallacin kamar yadda na yi alkawari, wannan yake karfafa ni”.

A nasa jawabin, mai martaba sarkin Musulmi kuma shugaban Majalisar Koli ta Addnin Musulunci, Sultan Muhammad Sa’ad Abubakar, ya yaba wa Gwamna a kan yadda ya yi alkawarin gina masallaci ya kuma cika alkawarin.

Ya kara da cewa, “Idan ka kalli yadda masallacin yake a da da kuma yadda ya zama a halin yanzu ba abin da zaka ce sai mika godiya ga Allah a kan rayuwar ‘Seyi Makinde a kan tunaninsa da kuma yadda ya aiwatar da tunanin nasa.

“Mutane da dama na furta alkawarin yin wani abu amma in an zo aiwatarwa sai kaga sun samu matsalar cika alkawarin da suka yi,” in ji shi.

Sultan ya kuma lakaba wa gwamnan na jihar Oyo sunansa na ‘Sa’ad’ a kan yadda ya yi alkawari na gina dakin Allah ya kuma cika alkawarin, ya ce, sabon masallacin wanda ke da makarantar Islamiya zai taimaka wa al’umma wajen samun ilimi duniya da na gobe kiyama.

Sultan ya kuma kara jaddada cewa, “Ana kira na Sa’ad, amma a yau zan sanya maka suna Sa’ad. Muna godiya ga Allah da ya kawo mu garin Ibadan muka halarci wannan al’amari mai matukar muhimmanci.

“Kusan shekara uku da suka wuce na yi magana da gwamnan, ya gaya mani cewa yana gina masallaci a wani wuri mai muhimmanci a garin Ibadan, na ce masa na san wurin, ya kuma ce, ni zan kaddamar da masallacin in an gama na kuma amsa masa cewa, lallai zan zo don kaddamarwar da yardar Allah.

“Na zagaya yankin gaba daya, ina mai tabbatar muku da cewa, babu wani gini da ya kai wannan masallacin kyau. Duk ta inda ka fito zaka ga masallacin abin da ya kamata mu rinka yi kenan ga al’ummarmu. Ya kamata mu rika gina dakunan Allah masu kyau.

“Masallaci ba wai wurin bauta kadai ba ne, ya kuma kasance makaranta. A yanzu mun samu makarantar Islamiyya da kyakyawar masallaci, abu ne da zai karfafa mana neman ilimin duniya da na lahira. Saboda haka ya kamata mu yi amfani da makarantar wajen ilimantar da kanmu, ‘yanuwanmu da sauran al’umma don mu zauna lafiya da juna ba tare da wata matsala ba.

“Wannan tarihi ne mai kyau muna fatan a samu irinsa a wurare da dama, saboda haka muna godiya ga mai girma Gwamna,” in ji Sultan Abubakar.

Daga karshe ya kuma nemi a tabbatar da kula da masallacin yadda ya kamata.

A nasu martanin, wasu al’umma Musulmi sun yaba wa Gwamnan Jihar Oyo, ‘Seyi Makinde, sun kwatanta shi da mai cika alkawari, sun ce basu taba tunanin zai cika allawarin da ya yi a shekarar 2019 na gina masallacin ba.

Wani mai sallah a masallacin, mai suna Mista Olawole Abdulfatah, ya ce, bai taba tunanin gwamnan zai cika alkawarin da ya yi ba, don ya yi tunanin alkawari ne irin na ‘yan siyasa da basa cikawa.

Shi kuwa wani mai suna Mista Ganiyu Adebayo, ya ce, kasancewar Saltan da sauran manyan manyan al’umma musulmi daga arewacin kasar nan wata manuniya ce na cewa, ana mutunta Gwamna Makinde a sassan Nijeriya saboda karfafa fatimtar juna a tsakanin kabilu da addinai a Nijeriya.

Wasu da suka yi jawabi a wajen taron sun bayyana cewa, hadin kai da zaman lafiya a tsakanin al’umma yana da matukar muhimmanci ga ci gaban Nijeriya. Sun kuma yaba wa Gwamna Makinde a bisa hangen nesansa na karfafa hadin kai da zaman lafiya ba wai na Jihar Oyo ba harma da Nijeriya baki daya.

Wadanda suka halarci taron sun hada da tsohon shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayyar Nijeriya, Alhaji Yayale Ahmed, manyan malaman addinin musulunci da manyan ma’aikatan gwamnati.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Mun Dakile Hari A Kano Da Ka Iya Zama Mafi Muni A Tarihin Nijeriya —Irabor
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Janar Irabor Ya Nemi A Sa Dokar Ta-baci A Wasu Sassan Nijeriya

October 17, 2025
Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
Rahotonni

Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya

October 11, 2025
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
Rahotonni

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

October 11, 2025
Next Post
Bayan Wata 3: Har Yanzu Al’umma Na Cikin Kunci Duk Da Tallafin Naira Biliyan 180 Ga Jihohi

Bayan Wata 3: Har Yanzu Al’umma Na Cikin Kunci Duk Da Tallafin Naira Biliyan 180 Ga Jihohi

LABARAI MASU NASABA

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

October 20, 2025
Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

October 20, 2025
Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.