• English
  • Business News
Saturday, November 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Noman Rani A Jihar Neja

by Abubakar Abba
2 years ago
Neja

Ministan Albarkatun Ruwa, Farfesa Joseph Terlumun Utseb, ya kaddamar da shirin noman rani; wanda aka yi wa lakabi da ‘Rafin-Yashi’.

Haka zalika, shirin ya kunshi samar da kadadar noma sama da guda 28 da kuma  gonar Songhai da ke karkashin hukumar kula da kogin Neja, domin kara habaka noman rani tare da lalubo  mafita a kan karancin abinci a fadin wannan kasa baki-daya.

  • NPA Ta Gargadi Masu Jibge Kwantaina Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Gwamnatin Kano Ta Dawo Da Ma’aikatan Da Ta Dakatar Da Ganduje Ya Ɗauka Aiki

Sannan Minsitan, ya kaddamar da tankunan ruwa sama da 700,000, wadanda za a iya adanawa tare da yin tanadin ruwa domin yin noman rani.

A cewar tasa, “daya daga cikin tankunan ruwan; za su rika yin amfani da shi wajen tura ruwa zuwa Rafin-Yashi, domin aiwatar da noman rani, inda sauran kuma za a rika amfani da su wajen tura ruwa zuwa gonar Songhai.

Har ila yau, Dam din Rafin Yashi, wanda guda ne cikin ayyukan da ministan ya kaddamar, ya kai zurfin kimanin kafa 650,000, wanda ko shakka babu zai yi matukar taimakawa; wajen rage ambaliyar ruwan sama a tsakanin al’ummar da ke zaune kusa da Dam din na Rafin Yashi,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

Ministan ya kara da cewa, idan aka kammala aikin wannan Dam, zai taimaka wajen samar da wutar lantarki da noman rani tare da taimakawa wajen kirkiro da ayyuakan yi da farfado da tattalin arzikin wannan kasa da kuma habaka samar da wadataccen abin abinci, wanda hakan ya yi daidai da kudire-kudiren Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu.

Bugu da kari, ya sanar da cewa, a makon da ya gabata; ma’aikatarsa ta kaddamar da ayyukan noman rani na shekarar 2023, domin bunkasa samar da wadataccen abinci  a fadin kasar.

Ministan ya kuma yi kira ga Gwamnatin Jihar Neja, ta samar da wadatacciyar kasa a Hukumar Kula da Kogin Neja, domin a rika yin noman rani, don amfanin jihar da kuma kasa baki-daya

Kazalika, ya sanar da cewa; akwai bukatar Gwamnatin Jihar ta samar da kayan aikin noman rani tare da bai wa ‘yan jihar kwarin guiwar rungumar yin ayyukan na noman rani, a cewar tasa wannan hanyar ce kadai za a kara samar da wadataccen abinci a fadin dukkanin wannan kasa.

Har wa yau ya kara da cewa, dole ne a samar da wadataccen abinci ga kafatanin ‘yan Nijeriya da kuma wanda za a rika fitarwa zuwa kasashen ketare.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Noma Da Kiwo

Shirin Shugaba Tinubu Na ‘Renewed Hope’ Zai Karfafa Wa Manoma Gwiwa – Oyebanji

November 7, 2025
An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi
Noma Da Kiwo

An Bukaci Manoma Su Rungumi Tsarin Noma Mai Jure Wa Sauyin Yanayi

November 7, 2025
Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci

November 2, 2025
Next Post
Yadda Ake Hada Turaren Hammata

Yadda Ake Hada Turaren Hammata

LABARAI MASU NASABA

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025
Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

Yadda Aka Tsara Gudanar Da Gasar Kofin Afirka A Moroko

November 8, 2025
CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Watsa Jerin Shirye-Shirye Don Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

CMG Ya Gabatar Da Jerin Rahotannin Talabijin Kan Tunawa Da Cika Shekaru 80 Da Dawowar Yankin Taiwan Kasar Sin

November 8, 2025
Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

Xi Ya Yi Kiran Zurfafa Gyare-gyare Da Bude Kofa A Yayin Rangadin Aiki A Guangdong

November 8, 2025
Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

Ta’aziyyar Rasuwar Jarumin Kannywood, Malam Nata’ala

November 8, 2025
Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

Kamfanoni Masu Jarin Waje Na Samun Kwarin Gwiwa Daga CIIE

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.