ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Noman Rani A Jihar Neja

by Abubakar Abba
3 years ago
Neja

Ministan Albarkatun Ruwa, Farfesa Joseph Terlumun Utseb, ya kaddamar da shirin noman rani; wanda aka yi wa lakabi da ‘Rafin-Yashi’.

Haka zalika, shirin ya kunshi samar da kadadar noma sama da guda 28 da kuma  gonar Songhai da ke karkashin hukumar kula da kogin Neja, domin kara habaka noman rani tare da lalubo  mafita a kan karancin abinci a fadin wannan kasa baki-daya.

  • NPA Ta Gargadi Masu Jibge Kwantaina Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Gwamnatin Kano Ta Dawo Da Ma’aikatan Da Ta Dakatar Da Ganduje Ya Ɗauka Aiki

Sannan Minsitan, ya kaddamar da tankunan ruwa sama da 700,000, wadanda za a iya adanawa tare da yin tanadin ruwa domin yin noman rani.

ADVERTISEMENT

A cewar tasa, “daya daga cikin tankunan ruwan; za su rika yin amfani da shi wajen tura ruwa zuwa Rafin-Yashi, domin aiwatar da noman rani, inda sauran kuma za a rika amfani da su wajen tura ruwa zuwa gonar Songhai.

Har ila yau, Dam din Rafin Yashi, wanda guda ne cikin ayyukan da ministan ya kaddamar, ya kai zurfin kimanin kafa 650,000, wanda ko shakka babu zai yi matukar taimakawa; wajen rage ambaliyar ruwan sama a tsakanin al’ummar da ke zaune kusa da Dam din na Rafin Yashi,” in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Ministan ya kara da cewa, idan aka kammala aikin wannan Dam, zai taimaka wajen samar da wutar lantarki da noman rani tare da taimakawa wajen kirkiro da ayyuakan yi da farfado da tattalin arzikin wannan kasa da kuma habaka samar da wadataccen abin abinci, wanda hakan ya yi daidai da kudire-kudiren Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu.

Bugu da kari, ya sanar da cewa, a makon da ya gabata; ma’aikatarsa ta kaddamar da ayyukan noman rani na shekarar 2023, domin bunkasa samar da wadataccen abinci  a fadin kasar.

Ministan ya kuma yi kira ga Gwamnatin Jihar Neja, ta samar da wadatacciyar kasa a Hukumar Kula da Kogin Neja, domin a rika yin noman rani, don amfanin jihar da kuma kasa baki-daya

Kazalika, ya sanar da cewa; akwai bukatar Gwamnatin Jihar ta samar da kayan aikin noman rani tare da bai wa ‘yan jihar kwarin guiwar rungumar yin ayyukan na noman rani, a cewar tasa wannan hanyar ce kadai za a kara samar da wadataccen abinci a fadin dukkanin wannan kasa.

Har wa yau ya kara da cewa, dole ne a samar da wadataccen abinci ga kafatanin ‘yan Nijeriya da kuma wanda za a rika fitarwa zuwa kasashen ketare.

Neja
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Tun Ina Karama Marigayi Tumbuleke Ke Sa Ni Dariya —Hannatu Musawa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    NPA Ta Bayyana Cewa Kirkiro Da Sabuwar Hukumar NPERA Ba Zai Zame Mata Tarnaki Ba
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Yadda Bikin Girke-girke Ya Karfafa Alaka Tsakanin Musulmai Da Kiristoci A Kaduna
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Wasu Dalilan Da Ke Haddasa Sabanin Abotakar Jarumi Ko Jaruma A Kannywood

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Yadda Ake Hada Turaren Hammata

Yadda Ake Hada Turaren Hammata

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.