Shugaban kasa, Bola Tinubu, zai gabatar da kasafin kudin shekarar 2024 a gaban majalisar tarayya nan da ‘yan Kwanaki.
Kakakin majalisar wakilai, Tajudeen Abbas, wanda ya bayyana hakan a wani taron karawa juna sani na kwana daya na shugabanni da mataimakan shugabannin zaunannen kwamitin majalisar a Abuja a ranar Litinin, ya kuma ce, majalisar wakilai za ta kira wani taron majalisar na masu ruwa da tsaki kan kasafin kudin shekarar 2024.
Shugaban majalisar ya bukaci shuwagabannin da mataimakan kwamitoci na majalisar da su yi nazari tare da kammala duk wani bincike kan kasafin cikin makonni biyu ba tare da yin gibi ko kawo wani cikas ga shirye-shiryen gabatar da kasafin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp