ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufar Sin Ta Baiwa Kasashe Damar Shigowa Kasarta Ba Tare Da Biza Ba Za Ta Bunkasa Mu’amala Tsakanin Jama’a Da Jama’a

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sanar a ranar 24 ga watan Nuwamba cewa, kasar Sin ta yanke shawarar gwada tsarin baiwa karin kasashe damar shiga kasar ba tare da biza ba, wanda ya shafi tsawaita zaman matafiya masu rike da fasfo na kasa da kasa daga kasashe shida, wato Faransa, Jamus, Italiya, Netherlands, Spain, da Malaysia.

Wato abin nufi shi ne, daga ranar 1 ga watan Disamba, 2023, zuwa ranar 30 ga watan Nuwamba, 2024, ’yan wadannan kasashe guda shida da ke shiga kasar Sin don kasuwanci, da yawon bude ido, da ziyartar ’yan uwa da abokan arziki, ko kuma yada zango na tsawon kwanaki 15, ba za su bukaci biza ba. Duk da cewa shirin na gwaji ne kamar yadda aka tsara. Amma idan shirin ya yi nasara kuma bai haifar da cikas ko wasu batutuwan da za su shafi zamantakewar al’umma ba, to ba mamaki shirin zai ci gaba da zama na dindindin.

  • Za Mu Samar Da Wutar Lantarki MW60 Ko Sola MW50 A Kowace Jiha -Gwamnonin Arewa Maso-Gabas
  • Tanzaniya Ta Yaba Wa Kasar Sin Game Da Hadin Gwiwa A Fannin Ilimin Fasaha Da Na Sana’a

Shirin yana da mahimmanci ta hanyoyi da yawa, yawancin tsarin shiga kasa ba tare da biza ba, ana gudanar da shi ne bisa tsarin hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, wanda ke nufin kasar mai shigowa ita ma dole ta tanadi kwatankwacin tsarin ga Sinawa.

ADVERTISEMENT

Hikimar dake cikin yadda kafofin watsa labaru suka fassara wannan matakin na Beijing shi ne, tsarin na da manufar jawo hankalin masu yawon bude ido daga wadannan kasashe. Saboda shekaru uku da aka yi ana fama da cutar ta COVID-19 ya yi tasiri sosai ga masana’antar yawon shakatawa ta duniya, saboda haka wannan manufa ce da za ta dora wannan fannin tattalin arziki bisa kyakkyawar turba.

A farkon watan Nuwamba, kasar Sin ta fadada manufofinta na yada zango a kasar ba tare da biza ba zuwa ga kasashe 54. Manyan jami’an gwamnatocin kasashen waje da suka hada da ministar harkokin wajen Faransa Catherine Colonna, da jakadiyar Jamus a kasar Sin Patricia Flor, sun yaba da wannan yunkurin inda suka yi tsokaci cewa, “Wannan yunkuri ne mai kyau kuma zai saukaka balaguro zuwa kasar Sin ga ’yan kasashen waje da dama da ba a taba ganin irinsa ba.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

A ganina, wannan sabon matakin ya wuce kawai don jawo hankalin masu yawon bude ido. Mataki ne dake nuni da yadda kasar Sin ta ci gaba da bude kofa ga kasashen duniya, da ci gaba da cudanya da sauran kasashen duniya, da ci gaba da yin mu’amala tsakanin jama’a da duniya. Fatana a nan shi ne a nan gaba, kasar Sin za ta shigar da karin kasashe masu tasowa cikin wannan tsarin musamman ma kasashen nahiyar Afirka. (Muhammed Yahaya)

 

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Sabon Nau’in Ciniki Dake Haifar Da Ci Gaba Ga Afrika Da Sin

Sabon Nau’in Ciniki Dake Haifar Da Ci Gaba Ga Afrika Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.