ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufar Sin Ta Baiwa Kasashe Damar Shigowa Kasarta Ba Tare Da Biza Ba Za Ta Bunkasa Mu’amala Tsakanin Jama’a Da Jama’a

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sanar a ranar 24 ga watan Nuwamba cewa, kasar Sin ta yanke shawarar gwada tsarin baiwa karin kasashe damar shiga kasar ba tare da biza ba, wanda ya shafi tsawaita zaman matafiya masu rike da fasfo na kasa da kasa daga kasashe shida, wato Faransa, Jamus, Italiya, Netherlands, Spain, da Malaysia.

Wato abin nufi shi ne, daga ranar 1 ga watan Disamba, 2023, zuwa ranar 30 ga watan Nuwamba, 2024, ’yan wadannan kasashe guda shida da ke shiga kasar Sin don kasuwanci, da yawon bude ido, da ziyartar ’yan uwa da abokan arziki, ko kuma yada zango na tsawon kwanaki 15, ba za su bukaci biza ba. Duk da cewa shirin na gwaji ne kamar yadda aka tsara. Amma idan shirin ya yi nasara kuma bai haifar da cikas ko wasu batutuwan da za su shafi zamantakewar al’umma ba, to ba mamaki shirin zai ci gaba da zama na dindindin.

  • Za Mu Samar Da Wutar Lantarki MW60 Ko Sola MW50 A Kowace Jiha -Gwamnonin Arewa Maso-Gabas
  • Tanzaniya Ta Yaba Wa Kasar Sin Game Da Hadin Gwiwa A Fannin Ilimin Fasaha Da Na Sana’a

Shirin yana da mahimmanci ta hanyoyi da yawa, yawancin tsarin shiga kasa ba tare da biza ba, ana gudanar da shi ne bisa tsarin hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, wanda ke nufin kasar mai shigowa ita ma dole ta tanadi kwatankwacin tsarin ga Sinawa.

ADVERTISEMENT

Hikimar dake cikin yadda kafofin watsa labaru suka fassara wannan matakin na Beijing shi ne, tsarin na da manufar jawo hankalin masu yawon bude ido daga wadannan kasashe. Saboda shekaru uku da aka yi ana fama da cutar ta COVID-19 ya yi tasiri sosai ga masana’antar yawon shakatawa ta duniya, saboda haka wannan manufa ce da za ta dora wannan fannin tattalin arziki bisa kyakkyawar turba.

A farkon watan Nuwamba, kasar Sin ta fadada manufofinta na yada zango a kasar ba tare da biza ba zuwa ga kasashe 54. Manyan jami’an gwamnatocin kasashen waje da suka hada da ministar harkokin wajen Faransa Catherine Colonna, da jakadiyar Jamus a kasar Sin Patricia Flor, sun yaba da wannan yunkurin inda suka yi tsokaci cewa, “Wannan yunkuri ne mai kyau kuma zai saukaka balaguro zuwa kasar Sin ga ’yan kasashen waje da dama da ba a taba ganin irinsa ba.

LABARAI MASU NASABA

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

A ganina, wannan sabon matakin ya wuce kawai don jawo hankalin masu yawon bude ido. Mataki ne dake nuni da yadda kasar Sin ta ci gaba da bude kofa ga kasashen duniya, da ci gaba da cudanya da sauran kasashen duniya, da ci gaba da yin mu’amala tsakanin jama’a da duniya. Fatana a nan shi ne a nan gaba, kasar Sin za ta shigar da karin kasashe masu tasowa cikin wannan tsarin musamman ma kasashen nahiyar Afirka. (Muhammed Yahaya)

 

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara
Daga Birnin Sin

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
Daga Birnin Sin

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Next Post
Sabon Nau’in Ciniki Dake Haifar Da Ci Gaba Ga Afrika Da Sin

Sabon Nau’in Ciniki Dake Haifar Da Ci Gaba Ga Afrika Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.