ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manufar Sin Ta Baiwa Kasashe Damar Shigowa Kasarta Ba Tare Da Biza Ba Za Ta Bunkasa Mu’amala Tsakanin Jama’a Da Jama’a

by CGTN Hausa
3 years ago
Sin

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta sanar a ranar 24 ga watan Nuwamba cewa, kasar Sin ta yanke shawarar gwada tsarin baiwa karin kasashe damar shiga kasar ba tare da biza ba, wanda ya shafi tsawaita zaman matafiya masu rike da fasfo na kasa da kasa daga kasashe shida, wato Faransa, Jamus, Italiya, Netherlands, Spain, da Malaysia.

Wato abin nufi shi ne, daga ranar 1 ga watan Disamba, 2023, zuwa ranar 30 ga watan Nuwamba, 2024, ’yan wadannan kasashe guda shida da ke shiga kasar Sin don kasuwanci, da yawon bude ido, da ziyartar ’yan uwa da abokan arziki, ko kuma yada zango na tsawon kwanaki 15, ba za su bukaci biza ba. Duk da cewa shirin na gwaji ne kamar yadda aka tsara. Amma idan shirin ya yi nasara kuma bai haifar da cikas ko wasu batutuwan da za su shafi zamantakewar al’umma ba, to ba mamaki shirin zai ci gaba da zama na dindindin.

  • Za Mu Samar Da Wutar Lantarki MW60 Ko Sola MW50 A Kowace Jiha -Gwamnonin Arewa Maso-Gabas
  • Tanzaniya Ta Yaba Wa Kasar Sin Game Da Hadin Gwiwa A Fannin Ilimin Fasaha Da Na Sana’a

Shirin yana da mahimmanci ta hanyoyi da yawa, yawancin tsarin shiga kasa ba tare da biza ba, ana gudanar da shi ne bisa tsarin hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu, wanda ke nufin kasar mai shigowa ita ma dole ta tanadi kwatankwacin tsarin ga Sinawa.

ADVERTISEMENT

Hikimar dake cikin yadda kafofin watsa labaru suka fassara wannan matakin na Beijing shi ne, tsarin na da manufar jawo hankalin masu yawon bude ido daga wadannan kasashe. Saboda shekaru uku da aka yi ana fama da cutar ta COVID-19 ya yi tasiri sosai ga masana’antar yawon shakatawa ta duniya, saboda haka wannan manufa ce da za ta dora wannan fannin tattalin arziki bisa kyakkyawar turba.

A farkon watan Nuwamba, kasar Sin ta fadada manufofinta na yada zango a kasar ba tare da biza ba zuwa ga kasashe 54. Manyan jami’an gwamnatocin kasashen waje da suka hada da ministar harkokin wajen Faransa Catherine Colonna, da jakadiyar Jamus a kasar Sin Patricia Flor, sun yaba da wannan yunkurin inda suka yi tsokaci cewa, “Wannan yunkuri ne mai kyau kuma zai saukaka balaguro zuwa kasar Sin ga ’yan kasashen waje da dama da ba a taba ganin irinsa ba.

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

A ganina, wannan sabon matakin ya wuce kawai don jawo hankalin masu yawon bude ido. Mataki ne dake nuni da yadda kasar Sin ta ci gaba da bude kofa ga kasashen duniya, da ci gaba da cudanya da sauran kasashen duniya, da ci gaba da yin mu’amala tsakanin jama’a da duniya. Fatana a nan shi ne a nan gaba, kasar Sin za ta shigar da karin kasashe masu tasowa cikin wannan tsarin musamman ma kasashen nahiyar Afirka. (Muhammed Yahaya)

 

Sin
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

MASU ALAKA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa
Daga Birnin Sin

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku
Daga Birnin Sin

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Next Post
Sabon Nau’in Ciniki Dake Haifar Da Ci Gaba Ga Afrika Da Sin

Sabon Nau’in Ciniki Dake Haifar Da Ci Gaba Ga Afrika Da Sin

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.