• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Bana: Alhazan Nijeriya 42,000 Da Sauran Alhazai Ne Suka Yi Tattaki Zuwa Dutsen Arafat

NAHCON ta nemi afuwar maniyatan da basu samu damar tashi zuwa kasa mai tsarki ba.

by Muhammad
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Hajjin Bana: Alhazan Nijeriya 42,000 Da Sauran Alhazai Ne Suka Yi Tattaki Zuwa Dutsen Arafat
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kimanin alhazai miliyan daya da suka hada da jimillar mutane 42,000 daga Nijeriya, sun hallara a Dutsen Arafat domin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2022 a ranar Juma’a.

Alhazan za su shafe tsawon yini guda a Dutsen Arafat a matsayin daya daga cikin manyan wuraren ibadar Hajji kafin su wuce zuwa Muzdalifah, inda za su kwana, sannan su koma Muna a ci gaba da gudanar da aikin hajji.

  • Al’ajabi: Yadda Wani Maniyyaci Ya Fara Aikin Hajjinsa A Sansanin Alhazai Na Kano Bayan Rasa Kujerarsa
  • Wani Dan Afrika Ta Kudu Ya Isa Birnin Makka Don Yin Aikin Hajji Bayan Shafe Tafiyar Shekaru 3

Tsayuwa a Arafa wani muhimmin bangare ne na aikin Hajji domin wuri ne da Allah yake karbar dukkan addu’o’in da mahajjata ke yi.

Ana sa ran mahajjata za su yi amfani da ranar don yin addu’o’i ga kansu, iyalai, abokai, al’uma, kasashe da duniya baki daya.

Dutsen Arafat kuma ana kiransa da Jabal ar-Rahmah, ma’ana dutsen rahama.

Labarai Masu Nasaba

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

A rana ta tara, mahajjata suna tashi daga Muna zuwa Dutsen Arafat inda suke tsaye cikin tawassuli da addu’o’i da karatun kur’ani.

A Dutsen Arafa ne Annabi Muhammad (S.A.W) ya yi hudubarsa ta karshe ga Musulmi wadanda suka raka shi aikin Hajji a karshen rayuwarsa.

Aikin Hajjin Mahajjaci ana ganin ba shi da inganci idan ba su yini ba a Dutsen Arafat.

A halin da ake ciki, Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta nemi afuwar daukacin alhazan Nijeriya na rashin samun Samar zuwa aikin hajjin 2022 da wahalhalu da rashin jin dadi da suka fuskanta a yayin da ake jigilar jiragen sama zuwa kasa mai tsarki a kasar Saudiyya.

Hukumar ta kuma nemi irin wannan afuwar ga gwamnatin tarayyar Nijeriya, da hukumomin jin dadin Alhazai na Jihohi da kamfanoni masu gudanar da jigilar Alhazai masu zaman kansu, da sauran jama’a kan duk wani abin rashin jin dadi da lamarin da ya faru a ‘yan makonnin da suka gabata ya jawo.

Hukumar ta bayar da hakuri na musamman ga maniyyata 1,552 da suka fito daga jihohin Bauchi, Filato da Kano da kuma wadanda ke karkashin masu gudanar da jigilar maniyyata ta Jiragen yawo da ba su samu damar zuwa wannan aikin Hajjin ba saboda koma bayan da aka samu a cikin mintunan karshe da ya kawo cikas ga shirinta na kammala jigilar alhazai kafin rufe filin jirgin sama na Jeddah. .

Alhazan da abin ya shafa sun hada da: maniyyata tara daga jihar Bauchi; Mahajjata 91 daga jihar Filato; Mahajjata 700 daga jihar Kano da kuma mahajjata kimanin 750 daga bangaren masu Jigila ta Jiragen yawo masu zaman kansu.

Hukumar a cikin wata sanarwa da ta fito daga mataimakiyar daraktarta kan harkokin jama’a, Hajiya Fatima Sanda Usara, ta tabbatar wa daukacin alhazan da abin ya shafa cewa za a mayar musu da kudin aikin Hajjinsu yayin da NAHCON za ta yi kokarin inganta nakasunta a shekarar 2023.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bukatar Gwamnati Ta Muhimmanta Jin Dadin ‘Yan Nijeriya

Next Post

Rashford Ya Ce Ya Koma Kan Ganiyarsa

Related

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

9 hours ago
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

12 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

16 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

19 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

1 day ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

1 day ago
Next Post
Rashford Ya Ce Ya Koma Kan Ganiyarsa

Rashford Ya Ce Ya Koma Kan Ganiyarsa

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.