ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Bana: Alhazan Nijeriya 42,000 Da Sauran Alhazai Ne Suka Yi Tattaki Zuwa Dutsen Arafat

NAHCON ta nemi afuwar maniyatan da basu samu damar tashi zuwa kasa mai tsarki ba.

by Muhammad
4 years ago
Hajji

Kimanin alhazai miliyan daya da suka hada da jimillar mutane 42,000 daga Nijeriya, sun hallara a Dutsen Arafat domin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2022 a ranar Juma’a.

Alhazan za su shafe tsawon yini guda a Dutsen Arafat a matsayin daya daga cikin manyan wuraren ibadar Hajji kafin su wuce zuwa Muzdalifah, inda za su kwana, sannan su koma Muna a ci gaba da gudanar da aikin hajji.

  • Al’ajabi: Yadda Wani Maniyyaci Ya Fara Aikin Hajjinsa A Sansanin Alhazai Na Kano Bayan Rasa Kujerarsa
  • Wani Dan Afrika Ta Kudu Ya Isa Birnin Makka Don Yin Aikin Hajji Bayan Shafe Tafiyar Shekaru 3

Tsayuwa a Arafa wani muhimmin bangare ne na aikin Hajji domin wuri ne da Allah yake karbar dukkan addu’o’in da mahajjata ke yi.

ADVERTISEMENT

Ana sa ran mahajjata za su yi amfani da ranar don yin addu’o’i ga kansu, iyalai, abokai, al’uma, kasashe da duniya baki daya.

Dutsen Arafat kuma ana kiransa da Jabal ar-Rahmah, ma’ana dutsen rahama.

LABARAI MASU NASABA

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

A rana ta tara, mahajjata suna tashi daga Muna zuwa Dutsen Arafat inda suke tsaye cikin tawassuli da addu’o’i da karatun kur’ani.

A Dutsen Arafa ne Annabi Muhammad (S.A.W) ya yi hudubarsa ta karshe ga Musulmi wadanda suka raka shi aikin Hajji a karshen rayuwarsa.

Aikin Hajjin Mahajjaci ana ganin ba shi da inganci idan ba su yini ba a Dutsen Arafat.

A halin da ake ciki, Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta nemi afuwar daukacin alhazan Nijeriya na rashin samun Samar zuwa aikin hajjin 2022 da wahalhalu da rashin jin dadi da suka fuskanta a yayin da ake jigilar jiragen sama zuwa kasa mai tsarki a kasar Saudiyya.

Hukumar ta kuma nemi irin wannan afuwar ga gwamnatin tarayyar Nijeriya, da hukumomin jin dadin Alhazai na Jihohi da kamfanoni masu gudanar da jigilar Alhazai masu zaman kansu, da sauran jama’a kan duk wani abin rashin jin dadi da lamarin da ya faru a ‘yan makonnin da suka gabata ya jawo.

Hukumar ta bayar da hakuri na musamman ga maniyyata 1,552 da suka fito daga jihohin Bauchi, Filato da Kano da kuma wadanda ke karkashin masu gudanar da jigilar maniyyata ta Jiragen yawo da ba su samu damar zuwa wannan aikin Hajjin ba saboda koma bayan da aka samu a cikin mintunan karshe da ya kawo cikas ga shirinta na kammala jigilar alhazai kafin rufe filin jirgin sama na Jeddah. .

Alhazan da abin ya shafa sun hada da: maniyyata tara daga jihar Bauchi; Mahajjata 91 daga jihar Filato; Mahajjata 700 daga jihar Kano da kuma mahajjata kimanin 750 daga bangaren masu Jigila ta Jiragen yawo masu zaman kansu.

Hukumar a cikin wata sanarwa da ta fito daga mataimakiyar daraktarta kan harkokin jama’a, Hajiya Fatima Sanda Usara, ta tabbatar wa daukacin alhazan da abin ya shafa cewa za a mayar musu da kudin aikin Hajjinsu yayin da NAHCON za ta yi kokarin inganta nakasunta a shekarar 2023.

Hajji
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano

MASU ALAKA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia
Manyan Labarai

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Next Post
Rashford Ya Ce Ya Koma Kan Ganiyarsa

Rashford Ya Ce Ya Koma Kan Ganiyarsa

LABARAI MASU NASABA

Hajji

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.