• Leadership Hausa
Sunday, August 7, 2022
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result
Home Labarai Manyan Labarai

Hajjin Bana: Alhazan Nijeriya 42,000 Da Sauran Alhazai Ne Suka Yi Tattaki Zuwa Dutsen Arafat

NAHCON ta nemi afuwar maniyatan da basu samu damar tashi zuwa kasa mai tsarki ba.

by Muhammad
1 month ago
in Manyan Labarai
0
Hajjin Bana: Alhazan Nijeriya 42,000 Da Sauran Alhazai Ne Suka Yi Tattaki Zuwa Dutsen Arafat
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kimanin alhazai miliyan daya da suka hada da jimillar mutane 42,000 daga Nijeriya, sun hallara a Dutsen Arafat domin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2022 a ranar Juma’a.

Alhazan za su shafe tsawon yini guda a Dutsen Arafat a matsayin daya daga cikin manyan wuraren ibadar Hajji kafin su wuce zuwa Muzdalifah, inda za su kwana, sannan su koma Muna a ci gaba da gudanar da aikin hajji.

  • Al’ajabi: Yadda Wani Maniyyaci Ya Fara Aikin Hajjinsa A Sansanin Alhazai Na Kano Bayan Rasa Kujerarsa
  • Wani Dan Afrika Ta Kudu Ya Isa Birnin Makka Don Yin Aikin Hajji Bayan Shafe Tafiyar Shekaru 3

Tsayuwa a Arafa wani muhimmin bangare ne na aikin Hajji domin wuri ne da Allah yake karbar dukkan addu’o’in da mahajjata ke yi.

Ana sa ran mahajjata za su yi amfani da ranar don yin addu’o’i ga kansu, iyalai, abokai, al’uma, kasashe da duniya baki daya.

Dutsen Arafat kuma ana kiransa da Jabal ar-Rahmah, ma’ana dutsen rahama.

Labarai Masu Nasaba

Luguden Ruwan Wuta Ya Kashe Kwamandan Boko Haram A Borno

Sojoji Sun Cafke ‘Yan Bindiga 7, Sun Kubutar Da Wasu Mutane

A rana ta tara, mahajjata suna tashi daga Muna zuwa Dutsen Arafat inda suke tsaye cikin tawassuli da addu’o’i da karatun kur’ani.

A Dutsen Arafa ne Annabi Muhammad (S.A.W) ya yi hudubarsa ta karshe ga Musulmi wadanda suka raka shi aikin Hajji a karshen rayuwarsa.

Aikin Hajjin Mahajjaci ana ganin ba shi da inganci idan ba su yini ba a Dutsen Arafat.

A halin da ake ciki, Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta nemi afuwar daukacin alhazan Nijeriya na rashin samun Samar zuwa aikin hajjin 2022 da wahalhalu da rashin jin dadi da suka fuskanta a yayin da ake jigilar jiragen sama zuwa kasa mai tsarki a kasar Saudiyya.

Hukumar ta kuma nemi irin wannan afuwar ga gwamnatin tarayyar Nijeriya, da hukumomin jin dadin Alhazai na Jihohi da kamfanoni masu gudanar da jigilar Alhazai masu zaman kansu, da sauran jama’a kan duk wani abin rashin jin dadi da lamarin da ya faru a ‘yan makonnin da suka gabata ya jawo.

Hukumar ta bayar da hakuri na musamman ga maniyyata 1,552 da suka fito daga jihohin Bauchi, Filato da Kano da kuma wadanda ke karkashin masu gudanar da jigilar maniyyata ta Jiragen yawo da ba su samu damar zuwa wannan aikin Hajjin ba saboda koma bayan da aka samu a cikin mintunan karshe da ya kawo cikas ga shirinta na kammala jigilar alhazai kafin rufe filin jirgin sama na Jeddah. .

Alhazan da abin ya shafa sun hada da: maniyyata tara daga jihar Bauchi; Mahajjata 91 daga jihar Filato; Mahajjata 700 daga jihar Kano da kuma mahajjata kimanin 750 daga bangaren masu Jigila ta Jiragen yawo masu zaman kansu.

Hukumar a cikin wata sanarwa da ta fito daga mataimakiyar daraktarta kan harkokin jama’a, Hajiya Fatima Sanda Usara, ta tabbatar wa daukacin alhazan da abin ya shafa cewa za a mayar musu da kudin aikin Hajjinsu yayin da NAHCON za ta yi kokarin inganta nakasunta a shekarar 2023.

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bukatar Gwamnati Ta Muhimmanta Jin Dadin ‘Yan Nijeriya

Next Post

Rashford Ya Ce Ya Koma Kan Ganiyarsa

Related

Luguden Ruwan Wuta Ya Kashe Kwamandan Boko Haram A Borno
Da ɗumi-ɗuminsa

Luguden Ruwan Wuta Ya Kashe Kwamandan Boko Haram A Borno

9 hours ago
Sojoji Sun Cafke ‘Yan Bindiga 7, Sun Kubutar Da Wasu Mutane
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke ‘Yan Bindiga 7, Sun Kubutar Da Wasu Mutane

24 hours ago
Tarihi Da Wasu Boyayyun Abubuwa Game Da Garin Tafa
Manyan Labarai

Tarihi Da Wasu Boyayyun Abubuwa Game Da Garin Tafa

2 days ago
Hukumar NDLEA Ta Bankado dakunan Sarrafa Miyagun kwayoyi A Legas Da Anambra
Manyan Labarai

Hukumar NDLEA Ta Bankado dakunan Sarrafa Miyagun kwayoyi A Legas Da Anambra

2 days ago
Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya
Manyan Labarai

Sabon Yunkurin Murkushe Barazanar Tsaro A Nijeriya

3 days ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ware Biliyan 2.6 Domin Tsaron Abuja
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ware Biliyan 2.6 Domin Tsaron Abuja

4 days ago
Next Post
Rashford Ya Ce Ya Koma Kan Ganiyarsa

Rashford Ya Ce Ya Koma Kan Ganiyarsa

LABARAI MASU NASABA

Kidayar ‘Yan Nijeriya Ta 2023: Shugaba Buhari Zai Bude Taron Masu Ruwa Da Tsaki

Kidayar ‘Yan Nijeriya Ta 2023: Shugaba Buhari Zai Bude Taron Masu Ruwa Da Tsaki

August 7, 2022
Peter Obi Ba Zaiyi Nasarar Lashe Koda Rabin Jihar Nasarawa Ba – Inji Deji Adeyanju

Peter Obi Ba Zaiyi Nasarar Lashe Koda Rabin Jihar Nasarawa Ba – Inji Deji Adeyanju

August 7, 2022
Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas

Hukumar NIS Ta Cafke Masu Safaran Makamai 3 A Kurus Ribas

August 7, 2022
MDD Da Gwamnatocin Kasashe Daban-Daban Sun Sake Jaddada Tsayawa Ga Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

MDD Da Gwamnatocin Kasashe Daban-Daban Sun Sake Jaddada Tsayawa Ga Manufar Kasancewar Kasar Sin Daya Tak A Duniya

August 7, 2022
Naira Miliyan 5 Nake Nema Don Fansar Mahaifiyata – Mace Mai Safarar Kwayoyi

Naira Miliyan 5 Nake Nema Don Fansar Mahaifiyata – Mace Mai Safarar Kwayoyi

August 7, 2022
Wakilin Sin Ya Ki Amincewa Da Zargin Da Amurka Ta Yi Kan Manufofin Makamashin Nukiliyar Kasar Sin

Wakilin Sin Ya Ki Amincewa Da Zargin Da Amurka Ta Yi Kan Manufofin Makamashin Nukiliyar Kasar Sin

August 7, 2022
NDLEA Ta Cafke Tsohon Sojan Da Ke Wa ‘Yan Bindiga Safarar Miyagun Kwayoyi

NDLEA Ta Cafke Tsohon Sojan Da Ke Wa ‘Yan Bindiga Safarar Miyagun Kwayoyi

August 7, 2022
Sharhi: Yadda Kasar Amurka Ta Nuna Fuska Biyu A Kan Batun Taiwan

Sharhi: Yadda Kasar Amurka Ta Nuna Fuska Biyu A Kan Batun Taiwan

August 7, 2022
Matsalar Tsaro: An Gudanar Da Addi’oi Na Musamman A Yankin Funtuwa

Matsalar Tsaro: An Gudanar Da Addi’oi Na Musamman A Yankin Funtuwa

August 7, 2022
Cinikayyar Waje Ta Hajojin Sin Ta Bunkasa Da Kaso 10.4 Bisa Dari Cikin Watanni 7 Na Bana

Cinikayyar Waje Ta Hajojin Sin Ta Bunkasa Da Kaso 10.4 Bisa Dari Cikin Watanni 7 Na Bana

August 7, 2022
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.