ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 8, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Hajjin Bana: Alhazan Nijeriya 42,000 Da Sauran Alhazai Ne Suka Yi Tattaki Zuwa Dutsen Arafat

NAHCON ta nemi afuwar maniyatan da basu samu damar tashi zuwa kasa mai tsarki ba.

by Muhammad
4 years ago
Hajji

Kimanin alhazai miliyan daya da suka hada da jimillar mutane 42,000 daga Nijeriya, sun hallara a Dutsen Arafat domin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2022 a ranar Juma’a.

Alhazan za su shafe tsawon yini guda a Dutsen Arafat a matsayin daya daga cikin manyan wuraren ibadar Hajji kafin su wuce zuwa Muzdalifah, inda za su kwana, sannan su koma Muna a ci gaba da gudanar da aikin hajji.

  • Al’ajabi: Yadda Wani Maniyyaci Ya Fara Aikin Hajjinsa A Sansanin Alhazai Na Kano Bayan Rasa Kujerarsa
  • Wani Dan Afrika Ta Kudu Ya Isa Birnin Makka Don Yin Aikin Hajji Bayan Shafe Tafiyar Shekaru 3

Tsayuwa a Arafa wani muhimmin bangare ne na aikin Hajji domin wuri ne da Allah yake karbar dukkan addu’o’in da mahajjata ke yi.

ADVERTISEMENT

Ana sa ran mahajjata za su yi amfani da ranar don yin addu’o’i ga kansu, iyalai, abokai, al’uma, kasashe da duniya baki daya.

Dutsen Arafat kuma ana kiransa da Jabal ar-Rahmah, ma’ana dutsen rahama.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

A rana ta tara, mahajjata suna tashi daga Muna zuwa Dutsen Arafat inda suke tsaye cikin tawassuli da addu’o’i da karatun kur’ani.

A Dutsen Arafa ne Annabi Muhammad (S.A.W) ya yi hudubarsa ta karshe ga Musulmi wadanda suka raka shi aikin Hajji a karshen rayuwarsa.

Aikin Hajjin Mahajjaci ana ganin ba shi da inganci idan ba su yini ba a Dutsen Arafat.

A halin da ake ciki, Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta nemi afuwar daukacin alhazan Nijeriya na rashin samun Samar zuwa aikin hajjin 2022 da wahalhalu da rashin jin dadi da suka fuskanta a yayin da ake jigilar jiragen sama zuwa kasa mai tsarki a kasar Saudiyya.

Hukumar ta kuma nemi irin wannan afuwar ga gwamnatin tarayyar Nijeriya, da hukumomin jin dadin Alhazai na Jihohi da kamfanoni masu gudanar da jigilar Alhazai masu zaman kansu, da sauran jama’a kan duk wani abin rashin jin dadi da lamarin da ya faru a ‘yan makonnin da suka gabata ya jawo.

Hukumar ta bayar da hakuri na musamman ga maniyyata 1,552 da suka fito daga jihohin Bauchi, Filato da Kano da kuma wadanda ke karkashin masu gudanar da jigilar maniyyata ta Jiragen yawo da ba su samu damar zuwa wannan aikin Hajjin ba saboda koma bayan da aka samu a cikin mintunan karshe da ya kawo cikas ga shirinta na kammala jigilar alhazai kafin rufe filin jirgin sama na Jeddah. .

Alhazan da abin ya shafa sun hada da: maniyyata tara daga jihar Bauchi; Mahajjata 91 daga jihar Filato; Mahajjata 700 daga jihar Kano da kuma mahajjata kimanin 750 daga bangaren masu Jigila ta Jiragen yawo masu zaman kansu.

Hukumar a cikin wata sanarwa da ta fito daga mataimakiyar daraktarta kan harkokin jama’a, Hajiya Fatima Sanda Usara, ta tabbatar wa daukacin alhazan da abin ya shafa cewa za a mayar musu da kudin aikin Hajjinsu yayin da NAHCON za ta yi kokarin inganta nakasunta a shekarar 2023.

Hajji
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Cikin Shekaru 28, Kudiri Ƙasa Da 10 Sanatocin Zamfara Ta Arewa Suka Gabatar A Majalisa – Shinkafi
  • Muhammad
    2027: NNPP Ta Yi Wa Korarrun Mambobinta Afuwa, Ta Yi Alƙawarin Basu Tikitin Kai-tsaye
  • Muhammad
    Musulunci Na Fuskantar Barazana A Karƙashin Mulkin Tinubu — Datti Baba-Ahmed
  • Muhammad
    Kwankwaso Tamkar Tsuntsu Ne A Siyasa Da Yake Sauya Sheƙa Daga Nan Zuwa Can – Ganduje

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno
Manyan Labarai

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027
Manyan Labarai

ADC Na Zawarcin Gawuna Domin Ya Yi Wa Jam’iyyar Takarar Gwamnan Kano A 2027

June 7, 2026
Next Post
Rashford Ya Ce Ya Koma Kan Ganiyarsa

Rashford Ya Ce Ya Koma Kan Ganiyarsa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

Sojoji Sun Kama Mutane 5 Masu Kai Wa Ƴan Bindiga Bayanai A Neja

June 7, 2026
A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

A Ranar Wasa Kawai Ƴan Wasan Iran Zasu Na Shiga Amurka, Bayan Wasa Su Fice

June 7, 2026
An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

An Tallafa Wa Waɗanda Harin Ƴan Bindiga Ya Raba Da Muhallansu A Sakkwato

June 7, 2026
Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

Daliban Kasar Sin Na Rubuta Jarabawar Gaokao Ta Shekarar Bana

June 7, 2026
NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

NDC Za Ta Fitar Da Sunayen Ƴan Takarar Da Suka Tsallake Tantancewa Yau

June 7, 2026
Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

Yadda Sin Da Laos Suka Daukaka Dangantakarsu Zai Amfanawa Duniya Baki Daya

June 7, 2026
Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Dandalin CMG Karo Na 5 Zai Bude Sabon Babin Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

June 7, 2026
Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

Ngoshe: Boko Haram Ta Saki Mata da Yara 416 da Aka Sace A Borno

June 7, 2026
Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

Matsalar Tsaro: Sarkin Musulmi Ya Buƙaci ‘Yansanda Su Haɗa Kai Da Sarakuna

June 7, 2026
Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Sare Bishiyoyi A Harabar Gidan Talabijin Na Jihar

June 7, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.