• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Sace Fiye Da Mutum 100 A Zamfara: Kauyukan Da ‘Yan Bindiga Suka Sanya Wa Haraji Na Fuskantar Barazana

by Hussein Yero
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Bayan Sace Fiye Da Mutum 100 A Zamfara: Kauyukan Da ‘Yan Bindiga Suka Sanya Wa Haraji Na Fuskantar Barazana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

Masu iya magana na cewa,abin da ya ci Doma bai barin Awai: Harin da ‘yan Bindiga suka kai gami da sace mutane a yankin Masarautar Dan Sadau, sakamakon kin biyan kudin fansa Naira miliyan 120, na kada hantar mutanan sauran kauyukan a koda yaushe sakamakon kin biyan nasu kudin.

Kauyukan da aka sanya wa kudin fansar aikin gona suna da dama amma,a Kananan Hukumomin Maru, Shinkafa, Anka, Maradun,Tsafe da Kauran Namoda abin ya fi tsanani.

  • Majalisa Na Fuskantar Kalubalen Amincewa Da Kasafin Naira Tiriliyan 27.5 Na 2024
  • Basirar Henry Kissinger Abu Mai Daraja Ne Ga Amurka

Domin ko a yanzu haka ‘yan Bindiga su kai hari a garin Ruwan Dorawa a mako biyu da suka wuce, inda suka sace mutum 13, da kisan mutum daya, sai kuma a ranar Juma’ar da ta gabata suka shiga yankin Masarautar Dan Sadau su kai sace mutum sama 100 a cikin daren wayewar gari Asabar da ta gabata.

Halin da da mutane Kauyukan, Mutunji, Kwanar Dutsi, Sabon Garin Mahuta da Unguwar Kawo, suke ciki baya ga sace mutanensu sama da 150 da ‘yan Bindigar suka yi karkashin jagorancin shugaban ‘yan Bindiga na Yanki Masarautar Dan Sadau Damuna.

Ya zuwa yanzu dai sama da mutane da dama ne  suka dawo gidajansu sakamakon lokacin da ‘yan Bindiga suke tafiya da su suka fashe suka fantsama cikin daji.

Wannan ne ya yi sanadiyyar dawowar mutane da dama bayan kwana biyu da kai masu harin, amma har yanzu wasu na hannunsu wadanda ba a san adadin su ba.

Daya daga cikin wadanda ya kubuta daga hannun ‘yan bindigar da ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana wa wakilinmu cewa, “A lokacin da ‘yan bindiga suka kora mu daji cikin dare da yake mun san yadda dajin yake da inda Dawa ke shuke da ciyayi masu tsawon duk inda aka a zo mutum ya san wurin sai ya sabe a guje ta haka ne mafi yawanmu muka tsira a hannun ‘yan Bindiga.”

“Ya kum tabbatar mana da cewa, shin Damuna zai sake dawowa garuruwan kuma lallai ba za su ji da dadiba.

Ana haka a ranar Lahadi sai ga motocin sojoji sun shigo garin amma zuwa Liitin sun bar garin, wannan ya kara sanya mana fargaba rashin sojoji a gari. Wannan ne ya sa yanzu haka wasu ke niyyar barin garin tun da ‘yan Bindiga sun tabbatar da cewa za su dawo kuma babu wani jami’in tsaro a garin.

A ta bangaren Gwamnatin Jihar Zamfara kuwa, ta bakin Gwamna Dauda Lawal da ya samu wakilcin, Shugaban Ma’aikata na Gidan Gwamnati, Muktat Muhammad Luga ya bayyana cewa, gwamnatin na sane da abubuwan rashin jindadi dake faruwa na tsaro a sasan jihar, gwamnatin na iyaka kokarinta don shawo kan matsalar tsaron.

Don yanzu haka ana ba wa ‘yan Sa kai horo domin tunkarar ‘yan Bindiga a duk inda suke a fadin Jihar.

Bangaren jama’an tsaro kuwa, Kakakin rundunar ‘yansandan na Jihar Zamfara, ASP Yazidu Abubakar ya bayyana wa manema labarai cewa, Rundunar Sojoji ne ke kula ya yankin Dan Sadau inda aka sace mutane sama mutum 100, sune ya kamata mu tuntuba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsaka Mai Wuyar Da Masu Gidajen Burodi Ke Ciki A Kaduna – Yarima

Next Post

Na Fi Jin Dadin Rubutu Da Sassafe Ko Dare – Princess Mazadu

Related

‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

1 week ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

1 week ago
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

2 months ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

3 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

3 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

3 months ago
Next Post
Na Fi Jin Dadin Rubutu Da Sassafe Ko Dare – Princess Mazadu

Na Fi Jin Dadin Rubutu Da Sassafe Ko Dare – Princess Mazadu

LABARAI MASU NASABA

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.