ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Sace Fiye Da Mutum 100 A Zamfara: Kauyukan Da ‘Yan Bindiga Suka Sanya Wa Haraji Na Fuskantar Barazana

by Hussein Yero
3 years ago

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

Masu iya magana na cewa,abin da ya ci Doma bai barin Awai: Harin da ‘yan Bindiga suka kai gami da sace mutane a yankin Masarautar Dan Sadau, sakamakon kin biyan kudin fansa Naira miliyan 120, na kada hantar mutanan sauran kauyukan a koda yaushe sakamakon kin biyan nasu kudin.

Kauyukan da aka sanya wa kudin fansar aikin gona suna da dama amma,a Kananan Hukumomin Maru, Shinkafa, Anka, Maradun,Tsafe da Kauran Namoda abin ya fi tsanani.

  • Majalisa Na Fuskantar Kalubalen Amincewa Da Kasafin Naira Tiriliyan 27.5 Na 2024
  • Basirar Henry Kissinger Abu Mai Daraja Ne Ga Amurka

Domin ko a yanzu haka ‘yan Bindiga su kai hari a garin Ruwan Dorawa a mako biyu da suka wuce, inda suka sace mutum 13, da kisan mutum daya, sai kuma a ranar Juma’ar da ta gabata suka shiga yankin Masarautar Dan Sadau su kai sace mutum sama 100 a cikin daren wayewar gari Asabar da ta gabata.

Halin da da mutane Kauyukan, Mutunji, Kwanar Dutsi, Sabon Garin Mahuta da Unguwar Kawo, suke ciki baya ga sace mutanensu sama da 150 da ‘yan Bindigar suka yi karkashin jagorancin shugaban ‘yan Bindiga na Yanki Masarautar Dan Sadau Damuna.

Ya zuwa yanzu dai sama da mutane da dama ne  suka dawo gidajansu sakamakon lokacin da ‘yan Bindiga suke tafiya da su suka fashe suka fantsama cikin daji.

Wannan ne ya yi sanadiyyar dawowar mutane da dama bayan kwana biyu da kai masu harin, amma har yanzu wasu na hannunsu wadanda ba a san adadin su ba.

Daya daga cikin wadanda ya kubuta daga hannun ‘yan bindigar da ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana wa wakilinmu cewa, “A lokacin da ‘yan bindiga suka kora mu daji cikin dare da yake mun san yadda dajin yake da inda Dawa ke shuke da ciyayi masu tsawon duk inda aka a zo mutum ya san wurin sai ya sabe a guje ta haka ne mafi yawanmu muka tsira a hannun ‘yan Bindiga.”

“Ya kum tabbatar mana da cewa, shin Damuna zai sake dawowa garuruwan kuma lallai ba za su ji da dadiba.

Ana haka a ranar Lahadi sai ga motocin sojoji sun shigo garin amma zuwa Liitin sun bar garin, wannan ya kara sanya mana fargaba rashin sojoji a gari. Wannan ne ya sa yanzu haka wasu ke niyyar barin garin tun da ‘yan Bindiga sun tabbatar da cewa za su dawo kuma babu wani jami’in tsaro a garin.

A ta bangaren Gwamnatin Jihar Zamfara kuwa, ta bakin Gwamna Dauda Lawal da ya samu wakilcin, Shugaban Ma’aikata na Gidan Gwamnati, Muktat Muhammad Luga ya bayyana cewa, gwamnatin na sane da abubuwan rashin jindadi dake faruwa na tsaro a sasan jihar, gwamnatin na iyaka kokarinta don shawo kan matsalar tsaron.

Don yanzu haka ana ba wa ‘yan Sa kai horo domin tunkarar ‘yan Bindiga a duk inda suke a fadin Jihar.

Bangaren jama’an tsaro kuwa, Kakakin rundunar ‘yansandan na Jihar Zamfara, ASP Yazidu Abubakar ya bayyana wa manema labarai cewa, Rundunar Sojoji ne ke kula ya yankin Dan Sadau inda aka sace mutane sama mutum 100, sune ya kamata mu tuntuba.

Hussein Yero
+ postsBio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    ’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Abdulaziz Yari Ya Bukaci Limamai Su Ƙara Addu’a Kan Yaƙi Da Ƴan Bindiga A Zamfara
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Na Fi Jin Dadin Rubutu Da Sassafe Ko Dare – Princess Mazadu

Na Fi Jin Dadin Rubutu Da Sassafe Ko Dare – Princess Mazadu

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.