ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bayan Sace Fiye Da Mutum 100 A Zamfara: Kauyukan Da ‘Yan Bindiga Suka Sanya Wa Haraji Na Fuskantar Barazana

by Hussein Yero
3 years ago

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Masu iya magana na cewa,abin da ya ci Doma bai barin Awai: Harin da ‘yan Bindiga suka kai gami da sace mutane a yankin Masarautar Dan Sadau, sakamakon kin biyan kudin fansa Naira miliyan 120, na kada hantar mutanan sauran kauyukan a koda yaushe sakamakon kin biyan nasu kudin.

Kauyukan da aka sanya wa kudin fansar aikin gona suna da dama amma,a Kananan Hukumomin Maru, Shinkafa, Anka, Maradun,Tsafe da Kauran Namoda abin ya fi tsanani.

  • Majalisa Na Fuskantar Kalubalen Amincewa Da Kasafin Naira Tiriliyan 27.5 Na 2024
  • Basirar Henry Kissinger Abu Mai Daraja Ne Ga Amurka

Domin ko a yanzu haka ‘yan Bindiga su kai hari a garin Ruwan Dorawa a mako biyu da suka wuce, inda suka sace mutum 13, da kisan mutum daya, sai kuma a ranar Juma’ar da ta gabata suka shiga yankin Masarautar Dan Sadau su kai sace mutum sama 100 a cikin daren wayewar gari Asabar da ta gabata.

Halin da da mutane Kauyukan, Mutunji, Kwanar Dutsi, Sabon Garin Mahuta da Unguwar Kawo, suke ciki baya ga sace mutanensu sama da 150 da ‘yan Bindigar suka yi karkashin jagorancin shugaban ‘yan Bindiga na Yanki Masarautar Dan Sadau Damuna.

Ya zuwa yanzu dai sama da mutane da dama ne  suka dawo gidajansu sakamakon lokacin da ‘yan Bindiga suke tafiya da su suka fashe suka fantsama cikin daji.

Wannan ne ya yi sanadiyyar dawowar mutane da dama bayan kwana biyu da kai masu harin, amma har yanzu wasu na hannunsu wadanda ba a san adadin su ba.

Daya daga cikin wadanda ya kubuta daga hannun ‘yan bindigar da ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana wa wakilinmu cewa, “A lokacin da ‘yan bindiga suka kora mu daji cikin dare da yake mun san yadda dajin yake da inda Dawa ke shuke da ciyayi masu tsawon duk inda aka a zo mutum ya san wurin sai ya sabe a guje ta haka ne mafi yawanmu muka tsira a hannun ‘yan Bindiga.”

“Ya kum tabbatar mana da cewa, shin Damuna zai sake dawowa garuruwan kuma lallai ba za su ji da dadiba.

Ana haka a ranar Lahadi sai ga motocin sojoji sun shigo garin amma zuwa Liitin sun bar garin, wannan ya kara sanya mana fargaba rashin sojoji a gari. Wannan ne ya sa yanzu haka wasu ke niyyar barin garin tun da ‘yan Bindiga sun tabbatar da cewa za su dawo kuma babu wani jami’in tsaro a garin.

A ta bangaren Gwamnatin Jihar Zamfara kuwa, ta bakin Gwamna Dauda Lawal da ya samu wakilcin, Shugaban Ma’aikata na Gidan Gwamnati, Muktat Muhammad Luga ya bayyana cewa, gwamnatin na sane da abubuwan rashin jindadi dake faruwa na tsaro a sasan jihar, gwamnatin na iyaka kokarinta don shawo kan matsalar tsaron.

Don yanzu haka ana ba wa ‘yan Sa kai horo domin tunkarar ‘yan Bindiga a duk inda suke a fadin Jihar.

Bangaren jama’an tsaro kuwa, Kakakin rundunar ‘yansandan na Jihar Zamfara, ASP Yazidu Abubakar ya bayyana wa manema labarai cewa, Rundunar Sojoji ne ke kula ya yankin Dan Sadau inda aka sace mutane sama mutum 100, sune ya kamata mu tuntuba.

Hussein Yero
+ postsBio
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Tsaro: Gwamna Lawal Ya Jaddada Kudirin Yaki da ‘Yan Ta’adda Ba Tare Da Sulhu Ba
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Yaƙi Da Ta’addanci: Gwamnan Zamfara Ya Jinjina Wa Jami’an Tsaro Bisa Ƙwato Ɗarurruwan Shanu
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    ’Yan Bindiga Sun Sace Dattawan Zamfara 50 Yayin Taron Sulhu A Cikin Daji
  • Hussein Yero
    https://hausa.leadership.ng/author/hussein-yero/
    Ɗan Takarar Sanata A Zamfara Ya Koka Kan Yi Wa Rayuwarsa Barazana
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Na Fi Jin Dadin Rubutu Da Sassafe Ko Dare – Princess Mazadu

Na Fi Jin Dadin Rubutu Da Sassafe Ko Dare – Princess Mazadu

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

Na Sayar Da ’Ya’yana, Na Sace Wasu 19 – Wata Da Ake Zargi Da Safarar Yara

September 9, 2026
Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.