• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Tinubu Ya Zama Gwarzon Shekara Na Kamfanin LEADERSHIP

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Tinubu

Rukunin kamfanin LEADERSHIP ta shelanta zabar Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu a matsayin gwarzon shekarar 2023.

A wata sanarwar da kamfanin ta fitar dauke da sanya hannun shugaba, Zainab Nda-Ishaih a ranar Litinin, ta ce LEADERSHIP, ta zabi Tinubu ne saboda yadda ya jajirce ya dage wajen tsallake tulin kalubalen da suke gabansa a ciki da wajen jam’iyyarsa ta APC har ya zama halastaccen shugaban kasar Nijeriya a zaben watan Fabrairun 2023.

  • Tinubu Ya Sake Mika Ta’aziyyarsa Ga Iyalan Da Harin Bam Ya Rutsa A Tudun Biri, Kaduna 
  • Muna Fata Masu Talla A Kafafen Sada Zumunta Su Fadakar Kan Shirye-shiryen Tinubu Na Habaka Tattalin Arziki 

Sanarwar ta kuma yi nuni kan irin salon matsayar da Tinubu ya dauka duk da tulin wahalhalun da suke akwai musamman jim kadan bayan darewarsa karagar mulki na yunkurinsa na sake farfado da Nijeriya.

Bikin gabatar da lambar karramawa ta LEADERSHIP, na gudana ne a yayin babban taron mika lambar yabo da jawabai na LEADERSHIP, kuma wannan shi ne karo na 16 da jaridar ke gudanarwa. Kan hakan, ana zakulo jajirtattun ‘yan Nijeriya, hazikan ma’aikata, daidaiku, da kamfanonin da suka yi zarra a bangarori daban-daban domin karrama su.

Tsarin zabin wadanda za su amshi lambar yabon ya gudana ne a watan Nuwamba wanda manya-manyan jagororin (majalisar editoci) na jaridar da sashin kasuwanci hade da manbobin hukumar ba da shawarwari wadanda kwararru ne a bangarori daban-daban suka cimma.

LABARAI MASU NASABA

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Tinubu ya kasance tsohon sanata, gwamnan farar hula har na wa’adi biyu a Jihar Legas, kuma ya amshi lambar yabon LEADERSHIP sau biyu, ya taka gagarumar rawa wajen samun nasarar APC wanda hakan ya kawo karshen mulkin PDP na shekaru 16, inda APC din ta kwace ragamar a 2015.

Duk da rawar da ya taka, ya sha gwagwarmaya a jam’iyyar na tsawon shekara takwas daga bisani ya yi kukan kura har ya samu nasarar jan ragamar komai na jam’iyyar da ma kasar nan baki daya.

A lokacin da ya shelanta aniyarsa na fitowa takara, Tinubu ya fuskanci tirjiya da koma baya daga cikin jam’iyyarsa ciki har ma da jami’an gwamnati a wancan lokacin da aka yi ta kawo abubuwan da za su iya zame masa tarnaki ga samun nasarar zama shugaban kasa ciki, wanda suka hada da rikita-rikitar canza fasalin takardun kudi da aka yi domin dakile aniyarsa na zama shugaban kasa.

Daker gwamnatin Muhammadu Buhar ta hakura ta amince ta mara masa baya har zuwa lokacin da gwamnonin APC na arewa suka tursasa gwamnatin da a mika ragamar takarar Nijeriya zuwa ga yankin kudancin kasar nan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya
Manyan Labarai

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki
Ra'ayi Riga

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Next Post
Ministan Kudi

Akwai Yiwuwar Gwamnati Ta Kara Yawan Kasafin Kudin 2024 – Ministan Kudi

LABARAI MASU NASABA

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

Bikin Baje Kolin CIIE Zai Samarwa Najeriya Karin Damammaki

November 3, 2025
Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

Chadi Ta Rufe Iyakarta Da Nijeriya Bisa Dalilan Tsaro

November 3, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Illata Fararen Hula Tare Da Fatan Gaggauta Kawo Karshen Yaki A Sudan

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.