• English
  • Business News
Thursday, November 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Yasa Ba Mu Buga Sunan Lawan Da Akpabio Ba – INEC

by Sadiq
3 years ago
INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta bayar da bayani kan yadda ta ki fitar da sunayen ainihin wadanda suka lashe zaben ‘yan takarar sanata na jam’iyyar APC mai mulki a matakai guda biyu.

A cikin wani yanayi mai cike da cece-kuce, an rasa sunayen shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Lawan, tsohon ministan harkokin Neja Delta, Godswill Akpabio.

  • Mutane 880 Sun Kamu Da Korona A Ranar Asabar – NCDC
  • Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Warware Sabanin Siyasa A Yammacin Afirka Da Sahel Ta Hanyar Shawarwari

Bashir Machina da Udom Ekpoudom sun fito zaben fidda-gwani na sanata a Yobe ta Arewa da Akwa-Ibom ta Arewa maso Yamma wanda INEC ta shaida, sai dai sunayen Lawan da Akpabio APC ta mika wa hukumar.

Dangane da rade-radin nuna son kai da wani bangare na al’umma ke yi wa INEC, hukumar a wata sanarwa da ta fitar a ranar Asabar, ta ce an tafka kura-kurai a kan matakin da ta dauka.

Dangane da mazabun biyu, hukumar ta ce ta sauke ayyukan da kundin tsarin mulkin kasar ya ba ta na sanya ido kan harkokin kudaden jam’iyyun siyasa da zabukan fidda-gwani.

LABARAI MASU NASABA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

Hukumar ta INEC ta tsaya tsayin daka wajen amincewa da rahotannin ofisoshinta na jihohi dangane da zaben ‘yan majalisar dattawa na jam’iyyar APC a yankunan da abin ya shafa tare da kalubalantar mambobin da suka koka da su garzaya kotu.

“Dangane da zabukan fidda-gwani na ‘yan majalisar dattawan Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma da Yobe ta Arewa, hukumar ta tsaya kan rahoton sa ido da aka samu daga ofisoshinmu na jiha.

“Saboda haka, hukumar ba ta buga bayanan kowane dan takarar mazabar biyu ba sabanin rahoton jihar ba.

“A yanzu haka, hukumar ta na aiki tukuru a kan matsalolin biyu. Masu korafin suna da ‘yancin tunkarar babbar kotun tarayya domin neman hakkinsu kamar yadda sashe na 285 na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya 1999 da sashe na 29(5) da 84(14) na dokar zabe. 2022, ” in ji Festus Okoye.

Machina da Ekpoudom sun samu shiga rahoton ofisoshin jihohin Yobe da Akwa-Ibom na hukumar a lokacin da Lawan da Akpabio sun zage damtse wajen samun damar lashe tikitin takarar shugaban kasa na APC.

Yayin da Mista Akpabio ya janye takarar neman takarar shugaban kasa, Bola Tinubu, Mista Lawan ya sha kaye a hannun tsohon gwamnan na jihar Legas.

Ganin yadda ake ta cece-kuce a kan takardun da aka buga na wasu daga cikin ‘yan takarar shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da na gwamnoni, INEC ta ki buga sunayen ‘yan takarkarun da ake da matsala a yankunansu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump
Labarai

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
ISWAP Ta Kwance Motoci 4 Dauke Da Abincin ‘Yan Gudun Hijira A Borno 

ISWAP Ta Kwance Motoci 4 Dauke Da Abincin 'Yan Gudun Hijira A Borno 

LABARAI MASU NASABA

Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

An Kama Wani Mutum Kan Zargin Kashe Matarsa A Sakkwato

November 6, 2025
Amnesty International Ta Soki Tinubu Kan Yi Wa Masu Laifin Take Haƙƙin Ɗan Adam Afuwa

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Don Karɓo Rancen N1.15trn Don Cike Giɓin Kasafin Kuɗin 2025

November 6, 2025
Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

Jirgin Ƙasa Ya Murƙushe Direban Adaidaita Sahu Da Fasinja A Jos

November 6, 2025
Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

Osimhen Ya Kafa Tarihi A Gasar Zakarun Turai Bayan Zura Ƙwallo 3 A Ragar Ajax

November 6, 2025
Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata

November 6, 2025
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP

Majalisa Ta Ɗage Tantance Ministan Tinubu Saboda Rashin Rahoton Tsaro

November 6, 2025
Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

Mao Ning: Harka Da Kasar Sin Mabudi Ne Na Samun Damammaki

November 5, 2025
Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

Yadda Gwamna Lawal Ya Aiwatar Da Ayyukan Gina Zamfara Na Naira Biliyan 140

November 5, 2025
Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

Li Chenggang Ya Gana Da Tawagar Cinikayyar Kayan Noma Ta Amurka

November 5, 2025
Majalisar Dattawa

Majalisa Ta Amince Da Ɗaurin Shekaru 14 A Gidan Yari Ga Malamai Masu Cin Zarafin Mata A Jami’o’i

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.