ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Yasa Ba Mu Buga Sunan Lawan Da Akpabio Ba – INEC

by Sadiq
4 years ago
INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta bayar da bayani kan yadda ta ki fitar da sunayen ainihin wadanda suka lashe zaben ‘yan takarar sanata na jam’iyyar APC mai mulki a matakai guda biyu.

A cikin wani yanayi mai cike da cece-kuce, an rasa sunayen shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Lawan, tsohon ministan harkokin Neja Delta, Godswill Akpabio.

  • Mutane 880 Sun Kamu Da Korona A Ranar Asabar – NCDC
  • Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Warware Sabanin Siyasa A Yammacin Afirka Da Sahel Ta Hanyar Shawarwari

Bashir Machina da Udom Ekpoudom sun fito zaben fidda-gwani na sanata a Yobe ta Arewa da Akwa-Ibom ta Arewa maso Yamma wanda INEC ta shaida, sai dai sunayen Lawan da Akpabio APC ta mika wa hukumar.

ADVERTISEMENT

Dangane da rade-radin nuna son kai da wani bangare na al’umma ke yi wa INEC, hukumar a wata sanarwa da ta fitar a ranar Asabar, ta ce an tafka kura-kurai a kan matakin da ta dauka.

Dangane da mazabun biyu, hukumar ta ce ta sauke ayyukan da kundin tsarin mulkin kasar ya ba ta na sanya ido kan harkokin kudaden jam’iyyun siyasa da zabukan fidda-gwani.

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

Hukumar ta INEC ta tsaya tsayin daka wajen amincewa da rahotannin ofisoshinta na jihohi dangane da zaben ‘yan majalisar dattawa na jam’iyyar APC a yankunan da abin ya shafa tare da kalubalantar mambobin da suka koka da su garzaya kotu.

“Dangane da zabukan fidda-gwani na ‘yan majalisar dattawan Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma da Yobe ta Arewa, hukumar ta tsaya kan rahoton sa ido da aka samu daga ofisoshinmu na jiha.

“Saboda haka, hukumar ba ta buga bayanan kowane dan takarar mazabar biyu ba sabanin rahoton jihar ba.

“A yanzu haka, hukumar ta na aiki tukuru a kan matsalolin biyu. Masu korafin suna da ‘yancin tunkarar babbar kotun tarayya domin neman hakkinsu kamar yadda sashe na 285 na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya 1999 da sashe na 29(5) da 84(14) na dokar zabe. 2022, ” in ji Festus Okoye.

Machina da Ekpoudom sun samu shiga rahoton ofisoshin jihohin Yobe da Akwa-Ibom na hukumar a lokacin da Lawan da Akpabio sun zage damtse wajen samun damar lashe tikitin takarar shugaban kasa na APC.

Yayin da Mista Akpabio ya janye takarar neman takarar shugaban kasa, Bola Tinubu, Mista Lawan ya sha kaye a hannun tsohon gwamnan na jihar Legas.

Ganin yadda ake ta cece-kuce a kan takardun da aka buga na wasu daga cikin ‘yan takarar shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da na gwamnoni, INEC ta ki buga sunayen ‘yan takarkarun da ake da matsala a yankunansu.

MASU ALAKA

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027
Siyasa

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
INEC
Siyasa

Muna Da Yan Takarar Gwamna A Jihohi 28 Don Shiga Zaben 2027

September 6, 2026
Next Post
ISWAP Ta Kwance Motoci 4 Dauke Da Abincin ‘Yan Gudun Hijira A Borno 

ISWAP Ta Kwance Motoci 4 Dauke Da Abincin 'Yan Gudun Hijira A Borno 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.