ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Abin Da Yasa Ba Mu Buga Sunan Lawan Da Akpabio Ba – INEC

by Sadiq
4 years ago
INEC

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta bayar da bayani kan yadda ta ki fitar da sunayen ainihin wadanda suka lashe zaben ‘yan takarar sanata na jam’iyyar APC mai mulki a matakai guda biyu.

A cikin wani yanayi mai cike da cece-kuce, an rasa sunayen shugaban majalisar dattawa, Sanata Ahmad Lawan, tsohon ministan harkokin Neja Delta, Godswill Akpabio.

  • Mutane 880 Sun Kamu Da Korona A Ranar Asabar – NCDC
  • Kasar Sin Ta Yi Kira Da A Warware Sabanin Siyasa A Yammacin Afirka Da Sahel Ta Hanyar Shawarwari

Bashir Machina da Udom Ekpoudom sun fito zaben fidda-gwani na sanata a Yobe ta Arewa da Akwa-Ibom ta Arewa maso Yamma wanda INEC ta shaida, sai dai sunayen Lawan da Akpabio APC ta mika wa hukumar.

ADVERTISEMENT

Dangane da rade-radin nuna son kai da wani bangare na al’umma ke yi wa INEC, hukumar a wata sanarwa da ta fitar a ranar Asabar, ta ce an tafka kura-kurai a kan matakin da ta dauka.

Dangane da mazabun biyu, hukumar ta ce ta sauke ayyukan da kundin tsarin mulkin kasar ya ba ta na sanya ido kan harkokin kudaden jam’iyyun siyasa da zabukan fidda-gwani.

LABARAI MASU NASABA

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

Hukumar ta INEC ta tsaya tsayin daka wajen amincewa da rahotannin ofisoshinta na jihohi dangane da zaben ‘yan majalisar dattawa na jam’iyyar APC a yankunan da abin ya shafa tare da kalubalantar mambobin da suka koka da su garzaya kotu.

“Dangane da zabukan fidda-gwani na ‘yan majalisar dattawan Akwa Ibom ta Arewa maso Yamma da Yobe ta Arewa, hukumar ta tsaya kan rahoton sa ido da aka samu daga ofisoshinmu na jiha.

“Saboda haka, hukumar ba ta buga bayanan kowane dan takarar mazabar biyu ba sabanin rahoton jihar ba.

“A yanzu haka, hukumar ta na aiki tukuru a kan matsalolin biyu. Masu korafin suna da ‘yancin tunkarar babbar kotun tarayya domin neman hakkinsu kamar yadda sashe na 285 na kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya 1999 da sashe na 29(5) da 84(14) na dokar zabe. 2022, ” in ji Festus Okoye.

Machina da Ekpoudom sun samu shiga rahoton ofisoshin jihohin Yobe da Akwa-Ibom na hukumar a lokacin da Lawan da Akpabio sun zage damtse wajen samun damar lashe tikitin takarar shugaban kasa na APC.

Yayin da Mista Akpabio ya janye takarar neman takarar shugaban kasa, Bola Tinubu, Mista Lawan ya sha kaye a hannun tsohon gwamnan na jihar Legas.

Ganin yadda ake ta cece-kuce a kan takardun da aka buga na wasu daga cikin ‘yan takarar shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da na gwamnoni, INEC ta ki buga sunayen ‘yan takarkarun da ake da matsala a yankunansu.

MASU ALAKA

ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya
Siyasa

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
Siyasa

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere
Siyasa

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
Next Post
ISWAP Ta Kwance Motoci 4 Dauke Da Abincin ‘Yan Gudun Hijira A Borno 

ISWAP Ta Kwance Motoci 4 Dauke Da Abincin 'Yan Gudun Hijira A Borno 

LABARAI MASU NASABA

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.