• English
  • Business News
Saturday, October 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kauyukan Yawan Shakatawa Na Sin Na Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kauyukan Yawan Shakatawa Na Sin Na Jawo Hankalin Sassan Kasa Da Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Karin kauyukan kasar Sin masu bude kofa ga ’yan yawon bude ido na samun karbuwa, da jawo ra’ayin al’ummun kasashen duniya daban daban. A kwanan nan ma karin irin wadannan kauyuka 4, sun shiga jerin “Kauyuka Mafiya Kayatarwa” na duniya na shekarar 2023, bisa jadawalin hukumar lura da yawon bude ido ta MDD ko UNWTO.

Sabbin kauyukan da suka shiga jadawalin a wannan karo sun hada da Huangling na lardin Jiangxi, da Xiajiang na lardin Zhejiang, da Zhagana na lardin Gansu. Sai kuma Zhujiawan na lardin Shaanxi. Kafin su akwai kauyukan Yucun na lardin Zhejiang, da Xidi na lardin Anhui, wadanda tun a shekarar 2021 suka yi nasarar shiga jadawalin na hukumar UNWTO.

  • An Samu Karuwar Masu Rajistar Sabbin Sana’o’i A Kasar Sin
  • Kowa Ya Gyara Ya Sani

Har ila yau, akwai kauyen Dazhai na jihar Guangxi ta kabilar Zhuang mai cin gashin kanta, da Jingzhu dake karkashin birnin Chongqing, wadanda suka shiga jadawalin a shekarar 2022. Bisa hakan, kasar Sin mai irin wadannan kauyuka har guda 8, ta zamo ta daya a duniya a yawan “Kauyuka mafiya kayatarwa” na yawon shakatawa dake cikin jadawalin hukumar ta UNWTO.

Hakika yawon shakatawa muhimmin fanni ne na raya al’adu, da musayar su, da sada zumunta tsakanin al’ummun sassan duniya daban daban, kana wata dama ce ta nishadantarwa, da samar da kudaden shiga, da guraben ayyukan yi, wanda hakan ke raya tattalin arzikin duniya baki daya.

A fannin yawon shakatawa mai alaka da kauyuka kuwa, ma iya cewa hakan wata dama ce ta bunkasa ci gaban yankunan karkara dake sassa daban daban na duniya, kana hakan na baiwa al’ummun duniya damar kiyaye al’adun gargajiya da ake gada daga kaka da kakanni, ciki har da na kayayyaki, da wadanda ba na kayayyaki ba, da fannin noma, da kare kyakkyawan yanayin muhallin halittu da dai sauransu.

Labarai Masu Nasaba

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Ko shakka babu kasar Sin ta yi rawar gani a fannin inganta wannan sashe, musamman a shekarun baya bayan nan, inda har ma ma’aikatar raya al’adun kasa da yawon bude ido ta kasar, ta ce an kai ga kyautata kauyukan yawon bude ido a matakin kasa har guda 1,597, wanda hakan ya ingiza harkar bude ido a sassa daban daban na karkarar kasar.

Yayin da duniya ke mayar da hankali ga raya karin sassan tattalin arziki, da kyautata muhalli da muhallin halittu, fadada fannin yawon bude ido na kauyuka da Sin ke yi abun a yaba ne, kuma abun koyi ga kasashe masu tasowa da dama dake da irin wannan fifiko.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: JaoanKasuwancin sinSabbin kasuwanni
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda ‘Yansanda Suka Gano Kungiyar Fataucin Yara A Kano, Sun Cafke 9

Next Post

Tsaron Da Muke Fatan Gani A Duniya

Related

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

59 minutes ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

2 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

3 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

4 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

23 hours ago
Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki
Daga Birnin Sin

Xi Ya Taya Grand Duke Guillaume Na Luxembourg Murnar Hawa Karagar Mulki

24 hours ago
Next Post
Duniya

Tsaron Da Muke Fatan Gani A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

October 4, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.