• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken Digirin Cuwa-cuwa Na Kasashen Waje Ya Tayar Da Kura

by Bello Hamza
2 years ago
in Labarai
0
NUC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Binciken da wani dan jarida na kafar yada labarai ta intanet, Daily Nigeria ya gudanar a kan yadda ake samun shaidar karatun Digiri ta cuwa-cuwa cikin mako shida a wata Jami’ar Kwantano da ke kasar Benin ya tayar da kura a Nijeriya cikin wannan makon inda Ministan Ilimi ya ba da umarnin dakatar da tantance duk wata shaidar karatun Digiri daga kasashen Benin da Togo.

Wakazalika, binciken wanda ya dangana har da shiga tsarin bautar kasa (NYSC) ta amfani da shaidar karatun ba tare da wata matsala ba, ya kuma jaza wa wasu jami’o’in waje guda 18 da ke Nijeriya, inda aka dakatar da harkokinsu da bayar da shaidar karatunsu nan take.

  • Yadda ANA Ta Shugabanci Gangamin Saukaka Zuwa Hajjin 2024 A Nijeriya
  • Dangote Ya Sauko Daga Matsayin Attajirin Da Ya Fi Kudi A Afrika

Hukumar kula da jami’o’i (NUC) ta gargadi al’umma da su guji mu’amala da wadannan jami’o’in.
Huhukumar, ta fitar da cikakken sunayen jami’o’in da aka haramta takardar shaidar digirinsu, inda ta wallafa sunayensu a shafinta na Intanet, da suka hada da: 1. Jami’ar Kimiyya da Gudanarwa ta Port No-bo, Jamhuriyar Benin, da sauran cibiyoyin ta da ke Nijeriya. 2. Jami’ar Bolta, da ke Ghana, da sauran cibiyoyin ta a Nijeriya. 3. Jami’ar International Unibersity, Missouri, USA, Kano da Lagos, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 4. Jami’ar Collumbus, UK, tana aiki da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 5. Tiu In-ternational Unibersity, UK, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya.

Sauran su ne: 6. Jami’ar Pebbles, UK, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 7. London Edternal Studies UK, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 8. Jami’ar Pilgrims da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 9. Jami’ar Kirista ta Yammacin Afirka, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 10. Jami’ar EC-Council Unibersity, Amurka, da ke da reshe a Ikeja a Jihar Legas. 11. Kwaleji Concept (London), Ilorin, da duk wasu ci-biyoyin ta a Nijeriya.

Bugu da kari, matakin ya kuma shafi 12. Jami’ar Houdegbe ta Arewacin Amurka da ke Nijeriya. 13. Makarantar Kasuwanci ta Jami’ar Irish a London, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 14. Jami’ar Ilimi, Winneba, Ghana, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 15. Jami’ar Cape Coast, Ghana, da duk wasu ci-biyoyin ta a Nijeriya. 16. Jami’ar Gamayya ta Afrika, da ke Kwatano da duk wasu cibiyoyinta a Nijeriya. Sai Jami’ar Yammacin Pacific, Denber, Colorado, da ke da Cibiya a Owerri da kuma 18. Jami’ar Ebangel ta Amurka da Chudick Management Academic, da ke Legas.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

Binciken da aka gudanar tun da dadewa ya sa ake ta cece-kuce a kan yadda matasan kasar nan ke tafiya Kwatano suna kammala karatun Digiri cikin dan kankanin lokaci.

Sai dai yanzu bisa wannan sanarwa, ba a san ko ma’aikatar ilimin za ta fito ta wallafa sunayen Jami’o’in da ta amince da su ba a kasashen.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ilimijabun digiriNUC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasafin 2024 Na Tarayya Da Jihohi Naira Tiriliyan 44.9 A Faifai

Next Post

Kirsimati: ‘Yan Nijeriya 163,000 Suka Ci Gajiyar Tallafin Sufurin Gwamnati – Minista

Related

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

2 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

3 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

6 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

7 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

17 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

19 hours ago
Next Post
minista

Kirsimati: ‘Yan Nijeriya 163,000 Suka Ci Gajiyar Tallafin Sufurin Gwamnati – Minista

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.