ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ANA Ta Shugabanci Gangamin Saukaka Zuwa Hajjin 2024 A Nijeriya

by Leadership Hausa
2 years ago
hajji

Domin saukaka zuwa aikin Hajjin 2024 ga Musulmin Nijeriya, wani hadin gwiwa bisa jagorancin Sanata Ahmad Abubakar MoAllahyidi a karkashin inuwar Kungiyar Arewa New Agenda (ANA), ya kaddamar da gangamin da ya gudanar na musamman kan lamarin.

Wannan yunkuri ya yi duba na tsanaki a kan muhimman batutuwan da suka shafi farashin kujera da samun damar sauke farali, tare da ba da shawarar daukar matakai don saukaka matsalolin kudi da maniyyata ke fsukanta.

Yunkurin na ANA a cewar jagororin kungiyar, ya samu amincewa da cikakken goyon bayan shugabancin hukumar Hajji ta kasa (NAHCON), tun daga farko har zuwa karshe.

ADVERTISEMENT

An yi gangamin na ANA ne ta hanyar gudanar da wasu muhimman ayyuka a yankunan da suka hada da Arewa maso Yamma, Arewa maso Gabas, Arewa ta Tsakiya, da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja, inda aka hada malaman addini, masu ruwa da tsaki, da hukumomin alhazai na jihohi wuri guda, domin magance matsalolin da ke addabar maniyyata, gabanin cikar wa’adin biyan kudin aikin Hajji da aka sa da farko na ranar 31 ga Disamba.

  • Gwamna Lawal Ya Raba Kayan Noma Ga Manoman Arewacin Zamfara

Gangamin na ANA ya kunshi dabarun magance kalubale iri-iri da ke tasiri wajen samun damar zuwa aikin Hajji, da suka hada da masauki a kusa da Harami, tsarin ciyar da abinci, kudin harajin kasa, kudin jirgi, da kuma kudin hidindimu, wadanda duk suna ba da gudummawa ga kara tsadar kudin kujera ga maniyyata.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Masu ruwa da tsaki sun bayyana damuwarsu a yayin gudanar da gangamin, musamman game da damfarar da ake yi wa alhazai, jinkirin yada bayanai, da rashin isasshiyar wayar da kan al’ummar karkara dangane da sabbin ka’idoji da wa’adin biyan kudin Hajjin 2024.

Binciken da aka yi na yanki ya nuna yadda wasu jihohin ke kokarin cike kason kujerun da aka ware musu na aikin Hajji, yayin da wasu kuma ke fuskantar kalubale saboda hukuncin da kotu ta yanke da kuma jinkirin abubuwan da aka sa a gaba. An gano bukatar tsawaita wa’adin karshe da samar da tallafi a matsayin manyan shawarwarin da za su saukaka zuwa aikin Hajji.

Yankin Arewa ta tsakiya ya bayyana rashin samun cikakkun bayanai tare da ba da shawarar gudanar da gangamin ilmantarwa don cike gibin wayar da kan maniyyata musamman wadanda suke karkara.

Masu ruwa da tsaki sun bayar da shawarar a rubanya kokarin wayar da kan jama’a, da kara hada kai da cibiyoyin hada-hadar kudi don magance matsalolin biyan kudi, da kuma yin kira ga gwamnatoci da su ba da tallafin kudin aikin Hajji, da magance matsalolin da suka shafi zamba, inganta gudanar da ayyuka, da kuma tsare-tsare na adashin gata a kan lokaci.

Wani abin karfafa gwiwa, jami’an gwamnati a jihohi daban-daban da suka hada da Kano, Kebbi, Birnin Abuja, Zamfara, Kwara, da Nasarawa, sun bayyana gamsuwa kan matakan da gwamnatocinsu suka dauka na ganin an samu nasarar gudanar da aikin Hajjin 2024, tare da tabbatar da kudirinsu na magance kalubalen da ake fuskanta.

Sanata MoAllahyidi ya mika godiya kan goyon bayan da hukumar alhazai ta kasa da kuma hukumomin alhazai na jihohi daban-daban suka ba su, inda ya yaba da kokarinsu na hadin gwiwa wajen samar da hanyoyin saukaka zuwa aikin Hajjin 2024 sauki ga musulmin Nijeriya.

 

 

hajji
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu
  • Leadership Hausa
    Ikirarin Cewa Sanata Abdul’aziz Yari Abubakar, Marafan Sokoto, Nauyi Ne Ga Jihar Zamfara Da Jam’iyyar APC Ba Ta Da Tushe
  • Leadership Hausa
    Nazarin Kisan Gillar Da ‘Yan Kato Da Gora Suka Yi Wa Wani Matashi A Biniwe

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Kasafin 2024

Kasafin 2024 Na Tarayya Da Jihohi Naira Tiriliyan 44.9 A Faifai

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.