ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda ANA Ta Shugabanci Gangamin Saukaka Zuwa Hajjin 2024 A Nijeriya

by Leadership Hausa
3 years ago
hajji

Domin saukaka zuwa aikin Hajjin 2024 ga Musulmin Nijeriya, wani hadin gwiwa bisa jagorancin Sanata Ahmad Abubakar MoAllahyidi a karkashin inuwar Kungiyar Arewa New Agenda (ANA), ya kaddamar da gangamin da ya gudanar na musamman kan lamarin.

Wannan yunkuri ya yi duba na tsanaki a kan muhimman batutuwan da suka shafi farashin kujera da samun damar sauke farali, tare da ba da shawarar daukar matakai don saukaka matsalolin kudi da maniyyata ke fsukanta.

Yunkurin na ANA a cewar jagororin kungiyar, ya samu amincewa da cikakken goyon bayan shugabancin hukumar Hajji ta kasa (NAHCON), tun daga farko har zuwa karshe.

ADVERTISEMENT

An yi gangamin na ANA ne ta hanyar gudanar da wasu muhimman ayyuka a yankunan da suka hada da Arewa maso Yamma, Arewa maso Gabas, Arewa ta Tsakiya, da kuma Babban Birnin Tarayya Abuja, inda aka hada malaman addini, masu ruwa da tsaki, da hukumomin alhazai na jihohi wuri guda, domin magance matsalolin da ke addabar maniyyata, gabanin cikar wa’adin biyan kudin aikin Hajji da aka sa da farko na ranar 31 ga Disamba.

  • Gwamna Lawal Ya Raba Kayan Noma Ga Manoman Arewacin Zamfara

Gangamin na ANA ya kunshi dabarun magance kalubale iri-iri da ke tasiri wajen samun damar zuwa aikin Hajji, da suka hada da masauki a kusa da Harami, tsarin ciyar da abinci, kudin harajin kasa, kudin jirgi, da kuma kudin hidindimu, wadanda duk suna ba da gudummawa ga kara tsadar kudin kujera ga maniyyata.

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Masu ruwa da tsaki sun bayyana damuwarsu a yayin gudanar da gangamin, musamman game da damfarar da ake yi wa alhazai, jinkirin yada bayanai, da rashin isasshiyar wayar da kan al’ummar karkara dangane da sabbin ka’idoji da wa’adin biyan kudin Hajjin 2024.

Binciken da aka yi na yanki ya nuna yadda wasu jihohin ke kokarin cike kason kujerun da aka ware musu na aikin Hajji, yayin da wasu kuma ke fuskantar kalubale saboda hukuncin da kotu ta yanke da kuma jinkirin abubuwan da aka sa a gaba. An gano bukatar tsawaita wa’adin karshe da samar da tallafi a matsayin manyan shawarwarin da za su saukaka zuwa aikin Hajji.

Yankin Arewa ta tsakiya ya bayyana rashin samun cikakkun bayanai tare da ba da shawarar gudanar da gangamin ilmantarwa don cike gibin wayar da kan maniyyata musamman wadanda suke karkara.

Masu ruwa da tsaki sun bayar da shawarar a rubanya kokarin wayar da kan jama’a, da kara hada kai da cibiyoyin hada-hadar kudi don magance matsalolin biyan kudi, da kuma yin kira ga gwamnatoci da su ba da tallafin kudin aikin Hajji, da magance matsalolin da suka shafi zamba, inganta gudanar da ayyuka, da kuma tsare-tsare na adashin gata a kan lokaci.

Wani abin karfafa gwiwa, jami’an gwamnati a jihohi daban-daban da suka hada da Kano, Kebbi, Birnin Abuja, Zamfara, Kwara, da Nasarawa, sun bayyana gamsuwa kan matakan da gwamnatocinsu suka dauka na ganin an samu nasarar gudanar da aikin Hajjin 2024, tare da tabbatar da kudirinsu na magance kalubalen da ake fuskanta.

Sanata MoAllahyidi ya mika godiya kan goyon bayan da hukumar alhazai ta kasa da kuma hukumomin alhazai na jihohi daban-daban suka ba su, inda ya yaba da kokarinsu na hadin gwiwa wajen samar da hanyoyin saukaka zuwa aikin Hajjin 2024 sauki ga musulmin Nijeriya.

 

 

hajji
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 
Labarai

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo
Labarai

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Next Post
Kasafin 2024

Kasafin 2024 Na Tarayya Da Jihohi Naira Tiriliyan 44.9 A Faifai

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.