ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kirsimati: ‘Yan Nijeriya 163,000 Suka Ci Gajiyar Tallafin Sufurin Gwamnati – Minista

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
minista

Shugaban kwamitin aiwatar da shirin tallafin sufuri na karshen shekara na Shugaba Bola Tinubu, Dakta Dele Alake, ya bayyana cewa sama da fasinjoji 160,000 ne suka ci gajiyar shirin.

Alake, wanda kuma yake rike da mukamin ministan bunkasa ma’adanai, ya bay-yana hakan ne a cikin rahotonsa da aka gabatar a Jihar Legas.

  • Kirismeti: Kukah Ya Bukaci Tinubu Ya Kawo Karshen Kisan Al’umma
  • Majalisa Ta Amince Tinubu Ya Ciwo Bashin Naira Tiriliyan 7.5

Shirin wanda shugaba Tinubu ya kaddamar a ranar 19 ga watan Disamba ya shafi samar da zirga-zirga kyauta a hanyoyin jiragen kasan Nijeriya (NRC).

ADVERTISEMENT

Bugu da kari, shugaban kasa ya rage kashi 50 na kudin sufuri ga fasinjojin da ke tafiya a kan hanyoyi 30 da masu gudanar da zirga-zirtar bas a karkashin kungiyar ‘Ludury Bus Owners of Nigeria’ (ALBON).
Da yake bayyana yadda shirin ya gudana, Alake ya jaddada gagarumar nasarar da aka samu.
Ya bayyana cewa ragin sufuri da Shugaba Tinubu ya aiwatar ya samu gagarumar nasara bisa la’akari da yadda ‘yan Nijeriya suka jin dadin lamarin.

“Tun daga ranar 21 ga Disamba zuwa 31 ga Disamba, 2023, alkaluma sun nuna cewa hukumar kula da zirga-zirgar jiragen kasa ta dauki fasinjoji 71,000, yayin da motocin bas da ke aiki a karkashin ALBON sun dauki fasinjoji 77,122.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

“Bas 652 da suka taso daga Oshodi na Legas sun dauki mutum 15,766. Wannan yana nufin cewa fasinjoji 163,878 ne suka amfana daga tallafin sufurin karshen shekara na shugaban kasa a cikin kwanaki 10.
“A yayin da fasinjoji a jirgin kasa suka samu gudanar da zirga-zirga kyautan, san-nan kuma fasinjoji take tafiya a kan hanya suka samu rangwame na kashi 50.”

Alake ya ce shirin na nuni ne da yadda shugaban kasar ke tausayawa da kuma kaunar ’yan Nijeriya wadanda suka kuduri aniyar gudanar da tafiye-tafiye a karshen shekara.

Ministan ya ce shirin yana kuma da nufin rage wa ‘yan kasar matsalar kudi, wadanda a cewarsa suna fuskantar wasu kalubale na tattalin arziki saboda bala’in da duniya ke fama da shi da kuma wasu abubuwan cikin gida.
Ya kara da cewa kwamitin ya dauki wasu matakai na gyara domin magance wasu kurakuran da aka gano wajen aiwatar da shirin, kamar kara wasu hanyoyi guda bi-yu da kuma jawo wasu masu ruwa da tsaki na motocin bas.

minista
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Manzon Allah

Allah Ya Daukaka Ambaton Manzon Allah (SAW) A Duniya Da Lahira

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.