ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken Digirin Cuwa-cuwa Na Kasashen Waje Ya Tayar Da Kura

by Bello Hamza
2 years ago
NUC

Binciken da wani dan jarida na kafar yada labarai ta intanet, Daily Nigeria ya gudanar a kan yadda ake samun shaidar karatun Digiri ta cuwa-cuwa cikin mako shida a wata Jami’ar Kwantano da ke kasar Benin ya tayar da kura a Nijeriya cikin wannan makon inda Ministan Ilimi ya ba da umarnin dakatar da tantance duk wata shaidar karatun Digiri daga kasashen Benin da Togo.

Wakazalika, binciken wanda ya dangana har da shiga tsarin bautar kasa (NYSC) ta amfani da shaidar karatun ba tare da wata matsala ba, ya kuma jaza wa wasu jami’o’in waje guda 18 da ke Nijeriya, inda aka dakatar da harkokinsu da bayar da shaidar karatunsu nan take.

  • Yadda ANA Ta Shugabanci Gangamin Saukaka Zuwa Hajjin 2024 A Nijeriya
  • Dangote Ya Sauko Daga Matsayin Attajirin Da Ya Fi Kudi A Afrika

Hukumar kula da jami’o’i (NUC) ta gargadi al’umma da su guji mu’amala da wadannan jami’o’in.
Huhukumar, ta fitar da cikakken sunayen jami’o’in da aka haramta takardar shaidar digirinsu, inda ta wallafa sunayensu a shafinta na Intanet, da suka hada da: 1. Jami’ar Kimiyya da Gudanarwa ta Port No-bo, Jamhuriyar Benin, da sauran cibiyoyin ta da ke Nijeriya. 2. Jami’ar Bolta, da ke Ghana, da sauran cibiyoyin ta a Nijeriya. 3. Jami’ar International Unibersity, Missouri, USA, Kano da Lagos, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 4. Jami’ar Collumbus, UK, tana aiki da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 5. Tiu In-ternational Unibersity, UK, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Sauran su ne: 6. Jami’ar Pebbles, UK, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 7. London Edternal Studies UK, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 8. Jami’ar Pilgrims da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 9. Jami’ar Kirista ta Yammacin Afirka, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 10. Jami’ar EC-Council Unibersity, Amurka, da ke da reshe a Ikeja a Jihar Legas. 11. Kwaleji Concept (London), Ilorin, da duk wasu ci-biyoyin ta a Nijeriya.

Bugu da kari, matakin ya kuma shafi 12. Jami’ar Houdegbe ta Arewacin Amurka da ke Nijeriya. 13. Makarantar Kasuwanci ta Jami’ar Irish a London, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 14. Jami’ar Ilimi, Winneba, Ghana, da duk wasu cibiyoyin ta a Nijeriya. 15. Jami’ar Cape Coast, Ghana, da duk wasu ci-biyoyin ta a Nijeriya. 16. Jami’ar Gamayya ta Afrika, da ke Kwatano da duk wasu cibiyoyinta a Nijeriya. Sai Jami’ar Yammacin Pacific, Denber, Colorado, da ke da Cibiya a Owerri da kuma 18. Jami’ar Ebangel ta Amurka da Chudick Management Academic, da ke Legas.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Binciken da aka gudanar tun da dadewa ya sa ake ta cece-kuce a kan yadda matasan kasar nan ke tafiya Kwatano suna kammala karatun Digiri cikin dan kankanin lokaci.

Sai dai yanzu bisa wannan sanarwa, ba a san ko ma’aikatar ilimin za ta fito ta wallafa sunayen Jami’o’in da ta amince da su ba a kasashen.

digiri
Bello Hamza
+ postsBio
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Dole Ne Afirka Ta Zamanantar Da Sufurin Jiragen Ruwa —Ɗantsoho
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Yadda Oyetola Ya Ƙaddamar Da Babban Taron Ƙungiyar  PMAWCA A Legas
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Lokaci Ya Yi Da Matasan Nijeriya Za Su Ƙwato Ƙasarsu — Kwamred Yahaya Abdullahi
  • Bello Hamza
    https://hausa.leadership.ng/author/bello-hamza/
    Kamfanin Dangote Na Kara Karfafa Hadin Gwiwar Tattalin Arziki Da Jihar Neja

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
minista

Kirsimati: ‘Yan Nijeriya 163,000 Suka Ci Gajiyar Tallafin Sufurin Gwamnati – Minista

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.